ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fadar Shugaban Kasa Ta Nemi A Sake Shigar Da Koyar Da Aikin Noma A Makarantu

by Abubakar Abba and Sulaiman
5 months ago
Noma

Domin samun nasarar samar da wadataccen abinci a daukacin fadin kasar nan, fadar shugaban kasa, ta bukaci a sake shigar da koyon aikin noma a makarantun kasar nan, musamman domin karfafa samar da abincin da kuma daidaita fannnin tattalin arzikin kasar.

Mataimakin Shugaban Kasa, Sanata Kashim Shettima ne ya bayar da wannan shawara a jawabinsa, a wajen babban taron kungiyar manoma ta kasa (AFAN) da aka gudanar a Abuja.

  • Hukumar RUWASSA Ta Kudiri Aniyar Samar Da Ruwa A Fadin Jihar Katsina
  • Jam’iyyar NNPP Tayi Ɓatan Dabo A Tarkadar Zaɓen Cike Gurbi Na Kano

Shettima, wanda babban mai taimaka masa a fannin kiwon lafiya, Uju Rochas-Anwukah ya wakilce shi a wajen taron, ya sanar da cewa; akwai bukatar shigar da koyon aikin noma a makarantun kasar, ba wai kawai a matsayin darasi ba, amma domin a karfafa tare da kwadaitar da dalibai rungumar aikin noma.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, ya kamata a ware wurin yin noma a makarantun, domin a fara koyar da daliban yadda ake yin noma, musamman domin su dauki fannnian a matsayin hanyar samarwa da kansu kudaden shiga.

“Dole ne a sake shigar da koyon aikin noma a makarantun kasar nan a matsayin wani fanni na gargajiya, ba wai kawai darasin da ilimin aikin noma da aka sanya wa daliban a cikin manhajar karatunsu ba, “in ji Kashim.

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

“Ya kamata ‘ya’yanmu su taso da sanin cewa, ana samun kudaden shiga da dama a fannin aikin noma,” a cewar tasa.

Haka zalika, ya yi kira ga shugabanni da kuma sauran cibiyoyin kasar nan da su sanya fannin aikin noma kai tsaye, duba da cewa; fanni ne da ya kamata a runguma a daukacin matakan kasar.

Shettima ya ci gaba da cewa, an jima a kasar nan, ‘yan kasar na daukar fannin aikin noma tamkar wani zaBi na karshe, maimakon su dauke shi a matsayin fanni mai dogon zango.

Koda-yake, Kashim ya sanar da cewa; wannan tunanin, ba wai abu ne marar kyau ba, amma dai fanni ne da ke samar da ayyukan yi kai tsaye da kuma kara daga martaba da darajar kasar.

Shi ma a nasa jawabin a wajen taron, babban ministan tsaro, Janar Christopher Musa mai murabus ya sanar da cewa, manoman kasar nan na ci gaba da fuskantar kalubale na rashin tsaro.

Sai dai, ya ba su tabbacin cewa; gwamnatin tarayya na yin iya kokarinta, domin lalubo da mafita kan wannan matsalar, musamman domin a kare rayukansu.

Kazalika, ya bukaci manoman da su kai duk wani rahoto na barazanar rashin tsaro ga mahukuntan da suka dace, domin a dauki matakin kare rayukansu da kuma dukiyarsu, duba da cewa; suna bayar da gagarumar gundunmawa wajen noma amfanin gonar da zai wadaci kasar.

Shi kuwa, a nasa jawabin na maraba a wajen taron, shugaban kungiyar na kasa, Dakta Farouk Mudi, ya zayyano wasu daga cikin kalubale na sauyin yanayi da ke shafar fannin na aikin noma da tsadar kayan aikin noma, musamman da kuma rashin tsaro.

Kazalika, ya sanar da cewa; jinkirin saukar ruwan damina da ambaliyar ruwan sama da tsadar farashin takin zamani, na shafar fannin na aikin noman kasar.

Ya yi kira ga mahukuntan kasar, da su samar da ingantattun tsare-tsare da zuba jari, musamman domin a tsamo fannin daga durkushewa.

Ya kara da cewa, a shekarar 2025, an samu jinkirin saukar ruwan damina, wanda ya kai har kusan kwana 21, sai kuma aka samu ambaliyar ruwan sama, inda aka kiyasata cewa, ya lalata kadadar noma sama da 500,000 da aka shuka Shinkafa da kuma Masara.

A cewarsa, shekaru biyu da suka gabata, farashin takin zamani samfarin NPK, an sayar da buhu daya kan Naira 26,000; wanda kuma a yau ake sayar da buhu daya a kan sama da Naira 53,000.

Kazalika, ya sanar da cewa; farashin kayan feshin gona, sun karu zuwa kusan kashi 300 a cikin dari, ya kara da cewa; aikin noma ya yi tsada, sannan kuma dole ne mutane na bukatar abinci.

Bugu da kari, shugaban ya bayyana cewa; akwai kuma bukatar a kara haBaka fannin kiwon kasar, duba da irin kalubalen da fannin ke fuskanta.

“A Nijeriya, akwai dimbin dabbobi, inda ake da akalla Shanu miliyan 21, Tumakai miliyan 43 da Awakai miliyan 82, amma sai dai, kasar na kashe dala biliyan 1.5, kwatankwacin Naira tiriliyan 2.2, wajen shigo da Madarar Shanu cikin kasar,“ a cewarsa.

Sai dai, ya danganta wannan matsalar kan ci gaban da ake samu da afkuwar rikice-rikiece, a yankunan kasar da ake kiwon dabbobi.

Mudi ya ci gaba da cewa, a shekaru goma da suka gabata, saboda irin wadannan rikice-rikicen, musamman a tsakanin manoma da kuma fulani makiyaya, kungiyar ta kuma yi asarar rayuka sama da 10,000 da kadarorin da kudinsu ya kai na sama da Naira biliyan 500. “Mun kuma yi asarar sama da dabbobi miliyan uku da Barayin Shanu suka sace, tare da kuma yin asarar wasu da biyo bayan tafiya da su kiwon da ba a riga an tsara shi yadda ya kamata ba” in ji Mudi.

Kazalika, kungiyar ta kuma ayyana goyon bayanta ga tsaron fannin kiwon dabbobi na kasa wato, NLTP.

“Muna bukatar masu kiwon dabbobi a kasar, su rungumi yin kiwon na zamani, wato wanda ake killace dabbobin a waje daya, domin a kiwata su, ba tare da fuskantar wata barazana ta rashin tsaro ba,” in ji shugaban.

Ya kuma danga samar da tsaro a matsayin babban ginshikin da zai sanya fannin aikin noma ya kara bunkasa a kasar.

Shugaban ya kuma yi nuni da cewa, Nijeriya a duk shekara na kashe sama da dala biliyan goma, kwatankwacin Naira tiriliyan sha biyar, wajen shigo da kayan abinci zuwa cikin kasar nan, musamman Alkama da Siga da kuma Kifi.

Ya bayyana cewa, kamata ya yi a ce; wadannan kudaden na zuwa ne ga manoman kasar nan, inda ya buga misali da cewa; Nijeriya na shigo da tan da dama na Alkama a duk shekara tare da kuma shigo Siga da yawansa ya kai kashi 90.

Noma
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Matatar Ɗangote Ta Ƙaryata Iƙirarin Dillalan Man Fetur 
Noma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA
  • Sulaiman
    Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka
  • Sulaiman
    NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin
  • Sulaiman
    Xi Ya Yi Kira Da A Bunkasa Salon Zamanantarwa Na Sin Ta Hanyar Ingiza Kirkire-kirkiren Kimiyya Da Fasaha

MASU ALAKA

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 
Noma Da Kiwo

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
Next Post
Binciken CGTN: Karin Haraji Mafi Yawa Ya Haifar Da Gibin Ciniki Mafi Girma Kana Manufar Harajin Trump Ta Wargaje

Binciken CGTN: Karin Haraji Mafi Yawa Ya Haifar Da Gibin Ciniki Mafi Girma Kana Manufar Harajin Trump Ta Wargaje

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026
Xi Ya Yi Kira Da A Bunkasa Salon Zamanantarwa Na Sin Ta Hanyar Ingiza Kirkire-kirkiren Kimiyya Da Fasaha

Xi Ya Yi Kira Da A Bunkasa Salon Zamanantarwa Na Sin Ta Hanyar Ingiza Kirkire-kirkiren Kimiyya Da Fasaha

July 8, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

July 8, 2026
Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.