ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fadar Shugaban Kasa Ta Nemi A Sake Shigar Da Koyar Da Aikin Noma A Makarantu

by Abubakar Abba and Sulaiman
3 months ago
Noma

Domin samun nasarar samar da wadataccen abinci a daukacin fadin kasar nan, fadar shugaban kasa, ta bukaci a sake shigar da koyon aikin noma a makarantun kasar nan, musamman domin karfafa samar da abincin da kuma daidaita fannnin tattalin arzikin kasar.

Mataimakin Shugaban Kasa, Sanata Kashim Shettima ne ya bayar da wannan shawara a jawabinsa, a wajen babban taron kungiyar manoma ta kasa (AFAN) da aka gudanar a Abuja.

  • Hukumar RUWASSA Ta Kudiri Aniyar Samar Da Ruwa A Fadin Jihar Katsina
  • Jam’iyyar NNPP Tayi Ɓatan Dabo A Tarkadar Zaɓen Cike Gurbi Na Kano

Shettima, wanda babban mai taimaka masa a fannin kiwon lafiya, Uju Rochas-Anwukah ya wakilce shi a wajen taron, ya sanar da cewa; akwai bukatar shigar da koyon aikin noma a makarantun kasar, ba wai kawai a matsayin darasi ba, amma domin a karfafa tare da kwadaitar da dalibai rungumar aikin noma.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, ya kamata a ware wurin yin noma a makarantun, domin a fara koyar da daliban yadda ake yin noma, musamman domin su dauki fannnian a matsayin hanyar samarwa da kansu kudaden shiga.

“Dole ne a sake shigar da koyon aikin noma a makarantun kasar nan a matsayin wani fanni na gargajiya, ba wai kawai darasin da ilimin aikin noma da aka sanya wa daliban a cikin manhajar karatunsu ba, “in ji Kashim.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

“Ya kamata ‘ya’yanmu su taso da sanin cewa, ana samun kudaden shiga da dama a fannin aikin noma,” a cewar tasa.

Haka zalika, ya yi kira ga shugabanni da kuma sauran cibiyoyin kasar nan da su sanya fannin aikin noma kai tsaye, duba da cewa; fanni ne da ya kamata a runguma a daukacin matakan kasar.

Shettima ya ci gaba da cewa, an jima a kasar nan, ‘yan kasar na daukar fannin aikin noma tamkar wani zaBi na karshe, maimakon su dauke shi a matsayin fanni mai dogon zango.

Koda-yake, Kashim ya sanar da cewa; wannan tunanin, ba wai abu ne marar kyau ba, amma dai fanni ne da ke samar da ayyukan yi kai tsaye da kuma kara daga martaba da darajar kasar.

Shi ma a nasa jawabin a wajen taron, babban ministan tsaro, Janar Christopher Musa mai murabus ya sanar da cewa, manoman kasar nan na ci gaba da fuskantar kalubale na rashin tsaro.

Sai dai, ya ba su tabbacin cewa; gwamnatin tarayya na yin iya kokarinta, domin lalubo da mafita kan wannan matsalar, musamman domin a kare rayukansu.

Kazalika, ya bukaci manoman da su kai duk wani rahoto na barazanar rashin tsaro ga mahukuntan da suka dace, domin a dauki matakin kare rayukansu da kuma dukiyarsu, duba da cewa; suna bayar da gagarumar gundunmawa wajen noma amfanin gonar da zai wadaci kasar.

Shi kuwa, a nasa jawabin na maraba a wajen taron, shugaban kungiyar na kasa, Dakta Farouk Mudi, ya zayyano wasu daga cikin kalubale na sauyin yanayi da ke shafar fannin na aikin noma da tsadar kayan aikin noma, musamman da kuma rashin tsaro.

Kazalika, ya sanar da cewa; jinkirin saukar ruwan damina da ambaliyar ruwan sama da tsadar farashin takin zamani, na shafar fannin na aikin noman kasar.

Ya yi kira ga mahukuntan kasar, da su samar da ingantattun tsare-tsare da zuba jari, musamman domin a tsamo fannin daga durkushewa.

Ya kara da cewa, a shekarar 2025, an samu jinkirin saukar ruwan damina, wanda ya kai har kusan kwana 21, sai kuma aka samu ambaliyar ruwan sama, inda aka kiyasata cewa, ya lalata kadadar noma sama da 500,000 da aka shuka Shinkafa da kuma Masara.

A cewarsa, shekaru biyu da suka gabata, farashin takin zamani samfarin NPK, an sayar da buhu daya kan Naira 26,000; wanda kuma a yau ake sayar da buhu daya a kan sama da Naira 53,000.

Kazalika, ya sanar da cewa; farashin kayan feshin gona, sun karu zuwa kusan kashi 300 a cikin dari, ya kara da cewa; aikin noma ya yi tsada, sannan kuma dole ne mutane na bukatar abinci.

Bugu da kari, shugaban ya bayyana cewa; akwai kuma bukatar a kara haBaka fannin kiwon kasar, duba da irin kalubalen da fannin ke fuskanta.

“A Nijeriya, akwai dimbin dabbobi, inda ake da akalla Shanu miliyan 21, Tumakai miliyan 43 da Awakai miliyan 82, amma sai dai, kasar na kashe dala biliyan 1.5, kwatankwacin Naira tiriliyan 2.2, wajen shigo da Madarar Shanu cikin kasar,“ a cewarsa.

Sai dai, ya danganta wannan matsalar kan ci gaban da ake samu da afkuwar rikice-rikiece, a yankunan kasar da ake kiwon dabbobi.

Mudi ya ci gaba da cewa, a shekaru goma da suka gabata, saboda irin wadannan rikice-rikicen, musamman a tsakanin manoma da kuma fulani makiyaya, kungiyar ta kuma yi asarar rayuka sama da 10,000 da kadarorin da kudinsu ya kai na sama da Naira biliyan 500. “Mun kuma yi asarar sama da dabbobi miliyan uku da Barayin Shanu suka sace, tare da kuma yin asarar wasu da biyo bayan tafiya da su kiwon da ba a riga an tsara shi yadda ya kamata ba” in ji Mudi.

Kazalika, kungiyar ta kuma ayyana goyon bayanta ga tsaron fannin kiwon dabbobi na kasa wato, NLTP.

“Muna bukatar masu kiwon dabbobi a kasar, su rungumi yin kiwon na zamani, wato wanda ake killace dabbobin a waje daya, domin a kiwata su, ba tare da fuskantar wata barazana ta rashin tsaro ba,” in ji shugaban.

Ya kuma danga samar da tsaro a matsayin babban ginshikin da zai sanya fannin aikin noma ya kara bunkasa a kasar.

Shugaban ya kuma yi nuni da cewa, Nijeriya a duk shekara na kashe sama da dala biliyan goma, kwatankwacin Naira tiriliyan sha biyar, wajen shigo da kayan abinci zuwa cikin kasar nan, musamman Alkama da Siga da kuma Kifi.

Ya bayyana cewa, kamata ya yi a ce; wadannan kudaden na zuwa ne ga manoman kasar nan, inda ya buga misali da cewa; Nijeriya na shigo da tan da dama na Alkama a duk shekara tare da kuma shigo Siga da yawansa ya kai kashi 90.

Noma
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 
Noma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Binciken CGTN: Karin Haraji Mafi Yawa Ya Haifar Da Gibin Ciniki Mafi Girma Kana Manufar Harajin Trump Ta Wargaje

Binciken CGTN: Karin Haraji Mafi Yawa Ya Haifar Da Gibin Ciniki Mafi Girma Kana Manufar Harajin Trump Ta Wargaje

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.