• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakilin Sin Ya Bukaci Kwamitin Sulhu Da Ya Soke Takunkuman Da Ya Kakabawa Sudan Ta Kudu

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

Jiya Jumma’a mataimakin zaunannen wakilin kasar Sin dake MDD Dai Bing, ya gabatar da wani jawabi yayin taron tattaunawa kan batun kasar Sudan ta kudu da kwamitin sulhun majalisar ya kira, inda ya bukaci kwamitin sulhun, da ya gaggauta soke takunkuman hana jigilar makamai da ya kakabawa kasar Sudan ta kudu.

Dai Bing ya bayyana cewa, a halin da ake ciki yanzu, yanayin siyasa na Sudan ta kudu ya shiga wani sabon mataki mai muhimmanci, bangarori daban daban da suka sa hannu kan yarjejeniyar sake farfado da Sudan ta kudu, sun cimma ra’ayi daya da jadawalin tsawaita wa’adin mika mulki a kasar a watan jiya, shawarar da suka yanke ta dace da yanayin da ake ciki yanzu, kana za ta samar da zaman lafiya a kasar.

  • An Shirya Tattaunawar Tiangong Tsakanin ‘Yan Sama Jannatin Sin Da Matasan Afirka Cikin Nasara

Don haka, ya dace sauran kasashe duniya su fahimci matsalar da Sudan ta kudu take fuskantar, su fahimci shawarar da aka yanke, kada su yi amfani da shirya zabe a matsayin wata dabara ta daidaita daukacin hargitsi, kuma bai kamata a yi watsi da kokarin gudanar da tattaunawar shimfida zaman lafiya da bangarori daban daban na Sudan ta kudu suke yi ba.

Dai Bing ya kara da cewa, yanzu haka an yi nasarar yaye tare da jibge kashin farko na rundunar sojojin kasar Sudan ta kudu lami lafiya, wannan babban ci gaba ne da aka samu yayin tabbatar da yarjejeniyar sake farfado da kasar, matakin da ya alamta cewa, aikin shimfida zaman lafiya ta Sudan ta kudu, ya samu sabon ci gaba.

Amma takunkuman da kwamitin sulhun MDD ya kakabawa Sudan ta kudu, yana da illa ga rundunar sojojin Sudan ta kudu na samu makaman da take bukata domin gudanar da aikinta, don haka kasar Sin ta sake yin kira ga kwamitin sulhun majalisar, da ya mai da hankali kan bukatun Sudan ta kudu, ya gaggauta soke takukumnan da ya kakabawa kasar, don taimakawa Sudan ta kudu wajen kara karfinta na tabbatar da tsaro a kasar. (Mai fassarawa: Jamila daga CMG Hausa)

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi
Daga Birnin Sin

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori
Daga Birnin Sin

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Next Post
Sin

Fina-finan Nollywood 5 Da Suke Koyar Da Mu Hanyoyin Samun Kudi

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

October 16, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.