Manzon musammam na shugaban kasar Sin Xi Jinping, watau Shao Hong, ya halarci bikin rantsar da shugaban Jamhuriyar Congo Denis Sassou Nguesso, wanda ya gudana jiya Juma’a a fadar shugaban kasar da ke birnin Brazzaville.
Shao Hong, wanda shi ne mataimakin shugaban kwamitin majalisar bayar da shawarwari kan harkokin siyasa ta kasar Sin, ya halarci bikin rantsuwar ne bisa gayyatar shugaba Sassou Nguesso.
Yayin ganawarsa da shugaba Denis Sassou Nguesso, Shao Hong ya ce kasar Sin na daukar batun raya huldarta da Jamhuriyar Congo da muhimmanci, kuma a shirye take ta hada hannu da kasar wajen aiwatar da matsayar da shugabannin kasashen biyu suka cimma da zurfafa hadin gwiwar moriyar juna da sauke nauyin da ke wuyansu a matsayinsu na masu shugabantar dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afrika domin jagorantar raya dangantakar Sin da Afrika da karfafa goyon bayan juna a tsakaninsu da kuma karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa.
A nasa bangare, shugaba Denis Sassou Nguesso ya yaba sosai da dangantakar da ke tsakanin kasarsa da Sin, yana mai nanata cewa, kasarsa na girmama dadaddiyar abotar da ke tsakaninsu, kuma a shirye take ta hada gwiwa da Sin a bangarori daban-daban da karfafa tuntubar juna da hadin gwiwa kan manyan batutuwan da suka shafi duniya da kara inganta gina al’umma mai makoma ta bai daya ta kasashen biyu. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post