Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya ce kasar Sin ta kasance abokiyar hulda kuma abar dogaro a tarihin huldarta da nahiyar Afrika, yana cewa manufar diplomasiyyar kasar na nacewa ga tsayawa tare da kasashe masu tasowa da abokan hulda na Afrika.
Wang Yi ya bayyana haka ne jiya Juma’a yayin ganawarsa da Selma Ashipala-Musavyi, ministar harkokin waje da cinikayya ta kasar Namibia, a birnin Beijing.
A cewarsa, fadadawa da zurfafa hadin gwiwar Sin da Namibia sun dace da muradun al’ummominsu da ma raya huldar Sin da Afrika, kuma hakan na nuna kokarin kasashe masu tasowa na karfafa hadin gwiwarsu.
Wang Yi ya kara da cewa, a shirye Sin take ta hada hannu da Namibia domin ci gajiyar manufar soke haraji ta kasar Sin da bunkasa hadin gwiwarsu a muhimman bangarori kamar na aikin gona da rayuwar jama’a da inganta harkokin matasa.
A nata bangare, Selma Ashipala-Musavyi ta yaba da goyon bayan da Sin ta dade tana ba kasashen Afrika, tana cewa ba tare da la’akari da yadda duniya za ta kasance ba, kasarta za ta ci gaba da goyon bayan manufar Sin daya tak a duniya, kuma ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen inganta hadin gwiwar abota da ke tsakaninta da Sin. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post