Memban hukumar siyasa, kana direktan ofishin kula da harkokin waje na kwamitin tsakiyar jam’iyyar kwaminis ta Sin Wang Yi, ya gana da mashawarci ga shugaban kasar Faransa kan harkokin waje Emmanuel Bonne jiya Juma’a a birnin Beijing.
Yayin zantawar tasu Wang Yi ya bayyana cewa, jagorancin shugabannin kasashen biyu bisa manyan tsare-tsare, yana bayyana kyakkyawar dangantakar musamman ta kasashen biyu.
Sin da Faransa a matsayinsu na mambobin dindindin a kwamitin sulhun MDD, kuma manyan kasashe masu cin gashin kansu, suna da nauyin dake rataye a wuyansu, na kiyaye zaman lafiya, da kwanciyar hankali da ci gaban duniya.
Wang Yi, ya kara da cewa yana fatan bangaren Faransa zai rike manufar “kasancewar kasar Sin daya tak a duniya” bisa matakai masu amfani. Ya kuma yi fatan Faransa za ta taimakawa Tarayyar Turai, wajen kafa kyakkyawar fahimta game da Sin, da kuma daukar manufofin kasuwanci da tattalin arziki masu amfani masu bude kofa ga Sin.
A nasa bangaren, Bonne ya bayyana cewa, bangaren Faransa yana rike da manufar “kasancewar kasar Sin daya tak a duniya”, kuma yana fatan hadin gwiwa da bangaren Sin, wajen neman mafita daga rikice-rikicen duniya, kuma yana son taka rawa mai kyau, a fannin ciyar da tattaunawa da hadin gwiwa tsakanin Turai da Sin gaba. (Mai Fassara: Amina Xu)















Discussion about this post