ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Dakile Yunkurin Satar Shanu Tare Da Cafke Mutum Hudu A Sokoto

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
2 months ago
Sokoto

Rundunar ‘yansandan Nijeriya ta kama wasu mutum uku tare da kwato bindiga AK-47 da aka kera ba bisa ka’ida ba, harsasai, bindigogin gargajiya (dane guns), da kuma shanu 46 da aka sato a jerin ayyukan tsaro da aka gudanar a Jihar Sokoto.

A cewar wata sanarwa da Kakakin Rundunar ‘Yansanda, Ahmad Rufa’i, ya fitar a ranar Litinin, an gudanar da wadannan ayyuka ne tsakanin watan Afrilu zuwa Mayu a sassa daban-daban na jihar.

‘Yansanda sun ce aikin farko ya faru ne a ranar 29 ga Afrilu, lokacin da jami’ai na ofishin ‘yansanda na Gidan Madi suka samu bayanan sirri kan wasu mutane da ake zargi da ke yankin Tangaza.

ADVERTISEMENT

Bayan kara sintiri da binciken motoci a hanyar Tangaza zuwa Gidan Madi, an kama mutum uku da ake zargi.

A wani aiki kuma a ranar 3 ga Mayu, jami’an sashen yaki da garkuwa da mutane sun dakile harin satar shanu a kauyen Gidan Bubu da ke Karamar Hukumar Wamakko, bayan samun bayanan sirri cewa ‘yan bindiga sun mamaye kauyen suna harbi kan mai uwa da wabi.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

A yayin bin sawunsu, tawagar ta bi su har zuwa dajin Gidan Gawe a Karamar Hukumar Silame, inda ‘yan bindigar suka tsere bayan musayar wuta, suka bar shanu 19 a baya.

Haka kuma rundunar ta ce an kwato shanu 27 a ranar 30 ga Afrilu bayan kiran gaggawa daga masu gadin al’umma a Tangaza, kan motsin wasu da ake zargi na kungiyar Lakurawa.

An gano shanun a kusa da kauyen Zamoriya bayan ‘yan bindigar sun gudu da zarar sun hango jami’an tsaro.

Kwamishinan ‘yansanda, Hayatu Hassan Shaffa, ya yaba wa jami’an da suka gudanar da ayyukan, tare da jaddada aniyar rundunar na yaki da rashin tsaro.

Ya ce irin wannan nasarori na nuna muhimmancin sahihan bayanan sirri da hadin gwiwa tsakanin al’umma da ‘yansanda, yana mai cewa ba za su gajiya ba har sai an kawar da miyagun mutane ko kuma an gurfanar da su a gaban shari’a.

Ya kuma yi kira ga mazauna Tangaza, Gidan Madi, Silame, Wamakko da Kware su ci gaba da ba da bayanai masu amfani ga hukumomin tsaro.

Rundunar ta kara da cewa ana ci gaba da bin sawun wadanda suka tsere domin gurfanar da su da kuma mayar da shanun ga ainihin masu su.

Sokoto
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu
Sokoto
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi
Tsaro

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

June 19, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Manyan Labarai

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
Next Post
Jimillar Cinikayyar Shige Da Fice Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 2.3% A Rubu’in Farko Na Bana

Jimillar Cinikayyar Shige Da Fice Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 2.3% A Rubu’in Farko Na Bana

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026
Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

June 23, 2026
'Yan Bindiga

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.