Bisa shawarar Sin, a matsayinta na kasa mai rike da shugabancin kwamitin sulhun MDD na wannan wata, a jiya Talata kwamitin sulhun ya gudanar da babban taro, game da “Kiyaye manufa da ka’idojin kundin mulkin MDD, da karfafa tsarin kasa da kasa bisa tushen MDD”.
Mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta Sin (JKS), kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi ne ya jagoranci taron, yayin da babban sakataren MDD Antonio Guterres ya gabatar da rahoto game da halin da ake ciki. Kazalika, wakilai daga kasashe sama da 100, ciki har da ministocin harkokin waje, da manyan wakilai sama da 20 sun halarci taron.
A cikin jawabinsa, Wang Yi ya bayyana cewa, a bana ake cika shekaru 55 tun bayan da jamhuriyyar jama’ar Sin ta dawo kan matsayinta na halal a MDD. A cikin shekaru 55 da suka gabata, Sin a matsayinta na mamba ta dindindin a kwamitin sulhu, ta shiga an dama da ita, cikin ayyukan ciyar da MDD gaba da cike da himma.
Har ila yau, tsaye a kan sabon mafari na tarihi, kasar Sin za ta ci gaba da sauke nauyin dake wuyanta, da bin hanya madaidaiciya tare da sauran kasashe, a karkashin ra’ayin cudanyar bangarori daban-daban na duniya, don samun hadin kai mai karfi, da gaggauta gina tsarin shugabancin duniya mafi adalci da daidaito, tare da gina kyakkyawar makomar bil-Adam ta bai daya cikin hadin gwiwa.
Da safiyar jiyan, Wang Yi ya gana da babban sakataren MDD Antonio Guterres, da ministocin harkokin waje na Bahrain, da Indonesia, sannan ya tattauna da manyan wakilai da suka halarci taron, ciki har da mataimakin ministan harkokin waje na Nicaragua, da mataimakin ministan harkokin waje na farko na kasar Kazakhstan. (Amina Xu)















Discussion about this post