Ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi, ya halarci wani taro na manyan jami’ai da aka shirya bisa cika shekaru biyar da gabatar da shawarar bunkasa ci gaban duniya (GDI), a birnin Beijing jiya Talata, inda ya yi kira ga kasashe da su ci gaba da riko da tambarin samun bunkasa da karfafa hadin gwiwa, kana su yi aiki tare domin gina makoma mai kyau.
Wang, wanda har ila yau memba ne a ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin (JKS), ya ce a yayin da ake fama da yanayin kasa da kasa mai sauyawa da ke cike da rudani, muhimmancin shawarar ta GDI ya kara fitowa fili. Yana mai kira ga kasashe da su kara himmar daidaita tsakanin shawarar GDI da ajandar samar da ci gaba ta Majalisar Dinkin Duniya.
Ya gabatar da shawarwari guda hudu domin inganta habaka ci gaban duniya. Na farko, Wang ya yi kira da a karfafa goyon bayan juna da hadin kai domin samar da yanayi na zaman lafiya don samun bunkasa. Na biyu, ya bukaci kasashe su yi aiki kafada-da-kafada domin hanzarta aiwatar da ajandar ci gaba mai dorewa ta shekarar 2030. Ya ce, kasar Sin za ta ci gaba da samar da karin albarkatu na ci gaba ga kasashe masu tasowa da kuma taimakawa wajen magance rashin daidaito da karancin abubuwan da ake bukata a bangaren ci gaban duniya.
Na uku kuwa, Wang ya yi kira da a bude kofa, a yi koyi da juna, da kuma samar da ci gaba ta hanyar kirkire-kirkire. Ya ce kasar Sin a shirye take ta zurfafa hadin gwiwa da dukkan bangarori wajen taimaka wa kasashe masu tasowa ta fuskar cin gajiyar sabbin damammaki da kuma magance kalubalen da ke tasowa. Na hudu, ya jaddada muhimmancin yin riko da tsarin damawa da mabambantan bangarori da kuma inganta jagoranci a duniya.
Yayin da yake nuni da cewa ba za a iya raba ci gaban kasar Sin da duniya ba, kuma shi kansa ci gaban duniya ma yana bukatar gudummawar kasar Sin. Wang ya jaddada cewa, duk irin yadda yanayin kasa da kasa ya sauya, kasar Sin za ta ci gaba da sauke nauyin da ya rataya a wuyanta a matsayinta na babbar kasa, tare da sada ci gabanta da na kasashen duniya bai-daya, da kuma taka rawar gani a matsayin mai karfafawa da kuma ba da gudummawa ga ci gaban duniya. (Mai Fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)














