Dakarun Sojin Shiyya 2 na Rundunar Haɗin Gwiwa ta Operation FANSAN YAMMA sun daƙile wasu yunƙurin garkuwa da mutane tare da ceto Shugaban Kwalejin Fasaha ta Tarayya da ke Kaura Namoda, Dakta Aminu Yusuf, da wasu mutane da dama a wasu hare-hare daban-daban da aka kai a Jihar Zamfara.
Rundunar sojin ta bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da Jami’in Yaɗa Labarai na ‘Operation FANSAN YAMMA’, Laftanar Kanal Aliyu Danja, ya wallafa a shafinsa na X a ranar Talata.
Sanarwar ta ce, harin farko ya faru ne da sanyin safiyar ranar 28 ga Yuli, lokacin da dakarun suka amsa kiran gaggawa kan wani harin da ‘yan ta’adda suka kai a yankin Titin Tsohon Tasha da ke Ƙaramar Hukumar Kaura Namoda.
A cewar Danja, maharan sun kutsa cikin gidan shugaban kwalejin, inda suka kashe jami’in tsaronsa tare da jikkata wani mazaunin gidan, kafin su yi yunƙurin yin garkuwa da Dakta Aminu Yusuf da iyalansa.
Ya ce, “Dakarun sun isa wurin cikin gaggawa tare da fafatawa da ‘yan ta’addan, lamarin da ya tilasta wa ‘yan ta’addan tserewa tare da barin waɗanda suka yi ƙoƙarin yin garkuwa da su. An ceto shugaban kwalejin da iyalansa cikin ƙoshin lafiya ba tare da sun ji rauni ba.”
Kakakin rundunar ya ƙara da cewa a wani samame da aka gudanar a wannan rana, dakarun da ke sintiri da dare sun amsa wani kiran gaggawa daga al’ummar Tungan Dorawa da ke ƙauyen Barkeji, inda ‘yan ta’adda ke ƙoƙarin yin garkuwa da mazauna yankin.
Ya ce duk da cewa, babu hanya mai kyau dake kaiwa ga al’ummar yankin, amma duk da haka, jami’an sun ci gaba da bibiyar maharan, inda suka fafata da su, tare da daƙile yunƙurin yin garkuwa da mutanen yankin.














