ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Wasika Ta Bayyana Kaunar Dake Tsakanin Sin Da Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Wasika

A kwanan baya, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya amsa wasikar da wasu tsoffin sojojin kasar Zimbabwe, wadanda suka taba halartar gwagwarmayar neman ’yancin kan kasar, suka rubuta masa, inda shugaban ya bayyana a cikin wasikarsa cewa, “Kasar Sin a ko da yaushe ita ce kawar kasashen Afirka, wadda ta samar da taimako ga yunkurin ’yantar da al’ummun Afirka, kuma tana kokarin hadin gwiwa da bangaren Afirka wajen neman ci gaban tattalin arziki da zamanantarwa.” Wannan magana, a ganina, ta nuna ma’anar huldar dake tsakanin Sin da Afirka.

Bayan da aka kafa jamhuriyar jama’ar kasar Sin a shekarar 1949, kasar ta samar da taimako ga al’ummun kasashen Afirka bisa yunkurinsu na neman ’yancin kan kasa, inda dimbin ’yan gwagwarmaya na Zimbabwe suka samu horo daga kasar Sin, lamarin da ya zama abun da ya cancanci tunawa a tarihin huldar kasashen Sin da Zimbabwe. A zahiri, ya kamata a yi kokarin gadon wannan hulda mai cike da kauna, ta yadda za mu iya amfani da ita wajen dakile yunkurin wasu kafofin yada labarai na kasashen yamma na samar da bahaguwar fahimta da neman lalata hulda a tsakanin al’ummun Sin da Afirka.

Sai dai zuwa yanzu, wani abu mai kyau da muka samu shi ne, muna iya ganin yadda huldar dake tsakanin Sin da Afirka ke ta kara karfi, bisa cudanyar mutane, da hadin gwiwa a fannin tattalin arziki da ake yi tsakaninsu. Misali, Issah Abiola, direba mace mai tuka jirgin kasa ta farko ta kasar Najeriya. Bayan da ta zama ma’aikaciyar wani kamfanin kasar Sin, ta samu damar koyon fasahar tuka jirgin kasa, har ma ta zama daya daga cikin direbobi masu tuka karamin jirgin kasa na birnin Abuja. Sa’an nan a nasa bangare, He Jie, wani dan wasan gudun dogon zango na kasar Sin, bayan da ya ga yadda mutanen kasar Kenya ke matukar kaunar wasan tsere na dogon zango, wannan batu ya burge shi sosai. Daga bisani, ya tafi kasar Kenya don neman samun horo sau da dama cikin shekaru 3 a jere, inda ya yi kokarin kyautata fasaharsa ta gudu, ta hanyar samun horo tare da dimbin fitattun ’yan wasa na kasashen Afirka. Zuwa yanzu, ya riga ya zama mai rike bajintar maza a wasan gudun Marathon ta kasar Sin.

ADVERTISEMENT

Ta wadannan misalai za mu iya ganin cewa, cudanyar da ake yi tsakanin mutanen kasar Sin da na kasashen Afirka tana haifar da ci gaban daidaikun mutane, da damar karfafa fahimtar juna, da amincewa da juna, da kauna, a tsakanin bangarorin Sin da Afirka.

Sa’an nan, a cikin wasikar da ya rubuta, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya ce shekarar 2026 ita ce shekarar “cudanyar mutane da musayar al’adu a tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka”. Wannan take ne na jerin ayyukan cudanya da aka tabbatar da su a taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka da ya gudana a birnin Beijing na kasar Sin a shekarar 2024, kuma yanzu ana aiwatar da ayyukan bisa shiri. An ce, za a gudanar da bukukuwa da yawansu ya kusan kai 600 a fannonin aikin ilimi, da al’adu, da yawon shakatawa, da dab’i, da wasannin motsa jiki, da dai sauransu, bisa hadin gwiwar bangarorin Sin da Afirka, inda za a samar da dandalin cudanya ga jama’ar bangarorin biyu, da damar kara kyautata hulda a tsakaninsu.

LABARAI MASU NASABA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ta wadannan bukukuwa, ake neman kula da ayyukan fannoni guda uku, wato ci gaban matasa, da rage talauci, gami da kimiyya da fasaha, ta yadda za a karfafa kauna da hadin kan al’ummun Sin da Afirka. Kana ta hanyar kokarin gadon kaunar da ta kasance tsakanin Sin da Afirka, dukkanmu za mu samar da gudunmowa ga yunkurin bangarorin Sin da Afirka na hadin gwiwa da juna a kokarin zamanantar da kansu. (Bello Wang)

Wasika
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Wasika
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • Sulaiman
    Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
  • Sulaiman
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

MASU ALAKA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Next Post
Shin Michael Carrick Ya Gyara Manchester United Ne?

Shin Michael Carrick Ya Gyara Manchester United Ne?

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.