ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Wasika Ta Bayyana Kaunar Dake Tsakanin Sin Da Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
Wasika

A kwanan baya, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya amsa wasikar da wasu tsoffin sojojin kasar Zimbabwe, wadanda suka taba halartar gwagwarmayar neman ’yancin kan kasar, suka rubuta masa, inda shugaban ya bayyana a cikin wasikarsa cewa, “Kasar Sin a ko da yaushe ita ce kawar kasashen Afirka, wadda ta samar da taimako ga yunkurin ’yantar da al’ummun Afirka, kuma tana kokarin hadin gwiwa da bangaren Afirka wajen neman ci gaban tattalin arziki da zamanantarwa.” Wannan magana, a ganina, ta nuna ma’anar huldar dake tsakanin Sin da Afirka.

Bayan da aka kafa jamhuriyar jama’ar kasar Sin a shekarar 1949, kasar ta samar da taimako ga al’ummun kasashen Afirka bisa yunkurinsu na neman ’yancin kan kasa, inda dimbin ’yan gwagwarmaya na Zimbabwe suka samu horo daga kasar Sin, lamarin da ya zama abun da ya cancanci tunawa a tarihin huldar kasashen Sin da Zimbabwe. A zahiri, ya kamata a yi kokarin gadon wannan hulda mai cike da kauna, ta yadda za mu iya amfani da ita wajen dakile yunkurin wasu kafofin yada labarai na kasashen yamma na samar da bahaguwar fahimta da neman lalata hulda a tsakanin al’ummun Sin da Afirka.

Sai dai zuwa yanzu, wani abu mai kyau da muka samu shi ne, muna iya ganin yadda huldar dake tsakanin Sin da Afirka ke ta kara karfi, bisa cudanyar mutane, da hadin gwiwa a fannin tattalin arziki da ake yi tsakaninsu. Misali, Issah Abiola, direba mace mai tuka jirgin kasa ta farko ta kasar Najeriya. Bayan da ta zama ma’aikaciyar wani kamfanin kasar Sin, ta samu damar koyon fasahar tuka jirgin kasa, har ma ta zama daya daga cikin direbobi masu tuka karamin jirgin kasa na birnin Abuja. Sa’an nan a nasa bangare, He Jie, wani dan wasan gudun dogon zango na kasar Sin, bayan da ya ga yadda mutanen kasar Kenya ke matukar kaunar wasan tsere na dogon zango, wannan batu ya burge shi sosai. Daga bisani, ya tafi kasar Kenya don neman samun horo sau da dama cikin shekaru 3 a jere, inda ya yi kokarin kyautata fasaharsa ta gudu, ta hanyar samun horo tare da dimbin fitattun ’yan wasa na kasashen Afirka. Zuwa yanzu, ya riga ya zama mai rike bajintar maza a wasan gudun Marathon ta kasar Sin.

ADVERTISEMENT

Ta wadannan misalai za mu iya ganin cewa, cudanyar da ake yi tsakanin mutanen kasar Sin da na kasashen Afirka tana haifar da ci gaban daidaikun mutane, da damar karfafa fahimtar juna, da amincewa da juna, da kauna, a tsakanin bangarorin Sin da Afirka.

Sa’an nan, a cikin wasikar da ya rubuta, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya ce shekarar 2026 ita ce shekarar “cudanyar mutane da musayar al’adu a tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka”. Wannan take ne na jerin ayyukan cudanya da aka tabbatar da su a taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka da ya gudana a birnin Beijing na kasar Sin a shekarar 2024, kuma yanzu ana aiwatar da ayyukan bisa shiri. An ce, za a gudanar da bukukuwa da yawansu ya kusan kai 600 a fannonin aikin ilimi, da al’adu, da yawon shakatawa, da dab’i, da wasannin motsa jiki, da dai sauransu, bisa hadin gwiwar bangarorin Sin da Afirka, inda za a samar da dandalin cudanya ga jama’ar bangarorin biyu, da damar kara kyautata hulda a tsakaninsu.

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

Ta wadannan bukukuwa, ake neman kula da ayyukan fannoni guda uku, wato ci gaban matasa, da rage talauci, gami da kimiyya da fasaha, ta yadda za a karfafa kauna da hadin kan al’ummun Sin da Afirka. Kana ta hanyar kokarin gadon kaunar da ta kasance tsakanin Sin da Afirka, dukkanmu za mu samar da gudunmowa ga yunkurin bangarorin Sin da Afirka na hadin gwiwa da juna a kokarin zamanantar da kansu. (Bello Wang)

Wasika
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Wasika
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 
Ra'ayi Riga

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
Next Post
Shin Michael Carrick Ya Gyara Manchester United Ne?

Shin Michael Carrick Ya Gyara Manchester United Ne?

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.