ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Wasika Ta Bayyana Kaunar Dake Tsakanin Sin Da Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
Wasika

A kwanan baya, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya amsa wasikar da wasu tsoffin sojojin kasar Zimbabwe, wadanda suka taba halartar gwagwarmayar neman ’yancin kan kasar, suka rubuta masa, inda shugaban ya bayyana a cikin wasikarsa cewa, “Kasar Sin a ko da yaushe ita ce kawar kasashen Afirka, wadda ta samar da taimako ga yunkurin ’yantar da al’ummun Afirka, kuma tana kokarin hadin gwiwa da bangaren Afirka wajen neman ci gaban tattalin arziki da zamanantarwa.” Wannan magana, a ganina, ta nuna ma’anar huldar dake tsakanin Sin da Afirka.

Bayan da aka kafa jamhuriyar jama’ar kasar Sin a shekarar 1949, kasar ta samar da taimako ga al’ummun kasashen Afirka bisa yunkurinsu na neman ’yancin kan kasa, inda dimbin ’yan gwagwarmaya na Zimbabwe suka samu horo daga kasar Sin, lamarin da ya zama abun da ya cancanci tunawa a tarihin huldar kasashen Sin da Zimbabwe. A zahiri, ya kamata a yi kokarin gadon wannan hulda mai cike da kauna, ta yadda za mu iya amfani da ita wajen dakile yunkurin wasu kafofin yada labarai na kasashen yamma na samar da bahaguwar fahimta da neman lalata hulda a tsakanin al’ummun Sin da Afirka.

Sai dai zuwa yanzu, wani abu mai kyau da muka samu shi ne, muna iya ganin yadda huldar dake tsakanin Sin da Afirka ke ta kara karfi, bisa cudanyar mutane, da hadin gwiwa a fannin tattalin arziki da ake yi tsakaninsu. Misali, Issah Abiola, direba mace mai tuka jirgin kasa ta farko ta kasar Najeriya. Bayan da ta zama ma’aikaciyar wani kamfanin kasar Sin, ta samu damar koyon fasahar tuka jirgin kasa, har ma ta zama daya daga cikin direbobi masu tuka karamin jirgin kasa na birnin Abuja. Sa’an nan a nasa bangare, He Jie, wani dan wasan gudun dogon zango na kasar Sin, bayan da ya ga yadda mutanen kasar Kenya ke matukar kaunar wasan tsere na dogon zango, wannan batu ya burge shi sosai. Daga bisani, ya tafi kasar Kenya don neman samun horo sau da dama cikin shekaru 3 a jere, inda ya yi kokarin kyautata fasaharsa ta gudu, ta hanyar samun horo tare da dimbin fitattun ’yan wasa na kasashen Afirka. Zuwa yanzu, ya riga ya zama mai rike bajintar maza a wasan gudun Marathon ta kasar Sin.

ADVERTISEMENT

Ta wadannan misalai za mu iya ganin cewa, cudanyar da ake yi tsakanin mutanen kasar Sin da na kasashen Afirka tana haifar da ci gaban daidaikun mutane, da damar karfafa fahimtar juna, da amincewa da juna, da kauna, a tsakanin bangarorin Sin da Afirka.

Sa’an nan, a cikin wasikar da ya rubuta, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya ce shekarar 2026 ita ce shekarar “cudanyar mutane da musayar al’adu a tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka”. Wannan take ne na jerin ayyukan cudanya da aka tabbatar da su a taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka da ya gudana a birnin Beijing na kasar Sin a shekarar 2024, kuma yanzu ana aiwatar da ayyukan bisa shiri. An ce, za a gudanar da bukukuwa da yawansu ya kusan kai 600 a fannonin aikin ilimi, da al’adu, da yawon shakatawa, da dab’i, da wasannin motsa jiki, da dai sauransu, bisa hadin gwiwar bangarorin Sin da Afirka, inda za a samar da dandalin cudanya ga jama’ar bangarorin biyu, da damar kara kyautata hulda a tsakaninsu.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Ta wadannan bukukuwa, ake neman kula da ayyukan fannoni guda uku, wato ci gaban matasa, da rage talauci, gami da kimiyya da fasaha, ta yadda za a karfafa kauna da hadin kan al’ummun Sin da Afirka. Kana ta hanyar kokarin gadon kaunar da ta kasance tsakanin Sin da Afirka, dukkanmu za mu samar da gudunmowa ga yunkurin bangarorin Sin da Afirka na hadin gwiwa da juna a kokarin zamanantar da kansu. (Bello Wang)

Wasika
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Wasika
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina Kasa

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Shin Michael Carrick Ya Gyara Manchester United Ne?

Shin Michael Carrick Ya Gyara Manchester United Ne?

LABARAI MASU NASABA

Wasika

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Wasika

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.