ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Michael Carrick Ya Gyara Manchester United Ne?

by Abba Ibrahim Wada
4 months ago
Carrick

Za a iya cewa an bude sabon shafi a kungiyar kwallon kafa ta Manchester United tun bayan korar mai koyarwa Ruben Amorim, bayan ya shafe watanni 14 yana koyar da kungiyar ta kasar Ingila.

Tun bayan nada Machael Carrick kociyan kungiyar na rikon kwarya abubuwa da dama suka canja musamman samun nasara a wasanni biyu a jere, kuma nasarar ta ban mamaki, domin manyan kungiyoyin Ingila, Manchester City da Arsenal ya doke, wadanda su ne a matsayi na daya da na biyu a halin yanzu a gasar Premier ta Ingila.

  • CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki
  • Gobara Ta Hallaka Mutum 2, Ta Lalata Dukiya Ta Biliyan 1.59 A Bauchi

Michael Carrick yana da kwarewar da ba za ta sa ya shagaltu ba kan cewa ko yana son zama kocin Manchester United na dindin, sai dai yana cike da farin ciki lokacin da ya bayyana cewa ‘yayansa sun halarci wasan kungiyarsa da Arsenal a filin wasa na Fly Emirates ranar Lahadi, inda suka shiga sahun dubban magoya baya da suka barke da murna lokacin da

ADVERTISEMENT

Matheus Cunha ya ci kwallon da ya bai wa United nasara da ci 3-2, kuma nasararsu ta farko kenan a gidan Arsenal cikin shekara takwas.

Sannan an nuno mai karamin hannun jari a Manchester United Sir Jim Ratcliffe cikin annashuwa lokacin da aka haska shi a Emirates. Babu lokuta da dama na yin murmushi sama da shekara biyu da ya sayi hannun jari a kungiyar ganin irin rashin katabus da suke yi.

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

Michael Carrick ya samu nasarar lashe wasanninsa na biyu tun fara jagoranci a United. Wani abu da Ruben Amorim ya taba samu sau daya cikin watanni 14 da ya yi a kungiyar – lokacin da ya samu nasarar wasanni uku a jere a farkon fara wannan kaka, abin da ya sa ya samu kyautar kocin da a fi kwazo na watan Oktoba.

Manchester United ta samu maki shida karkashin Carrick. Amorim kuwa ya shafe wasanni biyar kafin ya samu haka – inda daga nan ya yi rashin nasara a wasanni uku da suka bi baya.

Makonni shida da suka wuce, babu wanda zai zabi Carrick a matsayin kocin United na gaba a kan kocin Crystal Palace, Oliber Glasner. Amma yanzu akwai muryoyi da dama da suka gargadi United kan maimaita abin da ya faru a kakar wasa ta 2018 zuwa 2019.

Idan mai karatu bai manta ba, kakar wasanni bakwai da suka wuce, aka nada Ole Gunnar Solksjaer a matsayin kocin riko, ya lashe wasanni takwas a jere, sai kuma wasanni shida cikin tara da suka bi baya ya samu gagarumar nasara a hannun Paris sT-Germain a gasar Zakarun Turai, lokacin da United ta farfado daga kwallo biyu da PSG ta Parc des Princes – daga nan aka ba shi aikin kocin kungiyar na dindindin.

Solskjaer ya jagoranci Man United zuwa wasan karshe na gasar Europa a 2021, inda Billareal ta doke ta a bugun fenariti. Amma kuma samun nasarar wasanni na iya juyawa cikin gaggawa kamar yadda ra’ayoyi suka bayyana – duk da cewa Carrick bai nuna alamun za a ci United da sauki ba a yanzu.

Sai dai Carrick ya kawo sauyi na wasu matsaloli da aka samu lokacin Amorim – inda ya koma amfani da tsarin saka ‘yan wasa na 3-4-3 zuwa ‘yan wasa hudu a baya, da dawo da Kobbie Mainoo cikin tawagar da kuma mayar da kyaftin din kungiyar Bruno Fernandes komawa buga wasa can kusa da gaba, ba kamar lokacin Amorim ba.

Ya kuma wasu sauye-sauye masu karfi. Matakin da ya dauka na fara wasa da Patrick Dorgu a bangaren hagu na gaban Man United maimakon Matheus Cunha ya fara yin tasiri. Dorgu ya ci kwallo biyu a wasanni biyu karkashin Carrick, inda shi ma Cunha ya shiga fili ya ci wa United kwallo mai kyau da ta bai wa kungiyar nasara kan Arsenal da kuma bayar da kwallo a ci a wasansu da Manchester City.

Sai dai, duk da irin wannan namijin kokari da Michael Carrick ya fara da shi, tsoffin ‘yan wasan kungiyar Roy Keane da Gary Nebille, ba su amince cewa a ba shi aikin kocin kungiyar na dindindin ba. Makonni uku da suka wuce, Carrick yana can yana hutunsa tare da Wayne Rooney a tsibirin Barbados.

A ranar Juma’a, sun zauna tare a Old Trafford don kallon yadda Kai Rooney ya taimaka wa tawagar ‘yan kasa da shekara 18 na Man United zuwa zagayen 16 na FA Cup – ajin matasa.

Sai dai yanzu ana ganin shugabannin kungiyar za su fara tunanin ba wa tsohon dan wasan nasu aikin na dindindin musamman idan ya cikawa kungiyar burinta na zuwa kofin Zakarun Turai.

Manchester United kawo yanzu tana mataki na hudu a kan teburin gasar ta Ingila, maki 8 tsakaninta da kungiyoyin Manchester City da Aston Billa, wadanda suke mataki na biyu da na uku. Sannan akwai tazarar maki 12 tsakanin Manchester United da Arsenal, wadda take mataki na daya a gasar ta Ingila, ya yin da ya rage saura wasanni 15 a kamala kakar wasa ta bana.

Tun da farko shugabannin kungiyar sun bayyana cewa za su bawa Carrick rikon kwarya zuwa karshen kakar wasa ta bana, domin hakan zai basu damar nutsuwa su tattauna sannan su zabi mai koyarwar da za su dauka domin bashi ragamar koyar da kungiyar na dindindin, kamar dai yadda aka bawa Ruud Bannistlerooy koyar da kungiyar a baya kafin daukar Ruben Amorim.

Wasu daga cikin masu koyarwar da ake danganta kungiyar da su sun hada da Oliber Glasner, wanda zai bar kungiyar Crystal Palace a karshen kakar wasa ta bana, sai kuma Eddie Howe, kociyan kungiyar Newcastle United.

Akwai kuma kociyan tawagar Brazil, Carlo Ancelotti, da Thomas Tuchel, wanda yake koyar da tawagar ‘yanwasan Ingila, da kuma Mauricio Pochettino, wanda a yanzu yake koyar da tawagar ‘yanwasan kasar Amurka. Shima kociyan tawagar jamus, Nagelsman, yana cikin masu koyarwar da ake dangantawa da aikin koyar da Manchester United a kakar wasa mai zuwa.

Idan har Michael Carrick ya yi kokarin ganin kungiyar ta samu tikitin zuwa gasar cin kofin Zakarun Turai a kakar wasa mai zuwa tabbas zai cika jerin wadanda za a kalla wajen ba wa babban aikin.

Carrick
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
Xi Da Takwaransa Na Aljeriya Sun Taya Juna Murna Kan Nasarar Harba Tauraron Dan Adam Na Aljeriya

Xi Da Takwaransa Na Aljeriya Sun Taya Juna Murna Kan Nasarar Harba Tauraron Dan Adam Na Aljeriya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.