Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.
Jama’a barkanmu da sake kasancewa tare da ku a wannan fili namu mai albarka, filin da ke kawo muku batutuwan da suke ci wa al’umma tuwo a kwarya.
A wannan lokacin ina so na yi magana a kan wasu abubuwa guda biyu wadanda suke ci mana tuwo a kwarya a wannan rayuwar tamu.
Zan yi magana a kan shugabanci, ba mu dauke shi wani abin a zo a gani ba. Alal hakikanin gaskiya Allah subhnahu wa ta’ala ya ce a kangin kaina ma na haramta zalinci. Wato, shugabanni suna zaluntar mabiyansu.
Shugaba dai gabadaya idan aka yi magana akan shugabanci to, ka sani cewar lamari ne ubangiji ya ara maka, kuma ranar gobe alkiyama kowane shugaba zai je da ankwa, adalcin da yayi shi ne zai warware.
Shugaba shi ne madubi na tafiyar al’umma bakidaya, idan yayi adalci sai a ga al’ummar ta tafi daidai, kuma shi ma ya ga daidai. Tunda an kai kan wata gaba da lamurarrukan rayuwar ma kashi tamanin sai shugabanci na tafiya zai iya tafiyuwa yadda ya kamata.
Idanuwa suna rufewa wanda ba mu san lokacin da za mu mutu ba, amma da yawa shugabanni Allah yana ara musu rana, yana kuma basu dama.
To, muna fata kuma muna jan kunne ku sani Allah zai tsayar da ku, duk dukiyar da ka tara ko dai tsufa ya riske ka, ko kuma ka mutu ka bar wannan dukiya, kuma baka san me za a yi da ita ba. Daidai da naira daya duk yawan dukiyarka, in ka fi dan karuna arziki, ranar gobe alkiyama sai ka yi bayani “Ya akai ka same ta?, kuma da me ka sarrafata?”.
Sannan kowacce gaba ta jikin dan’adam sai ya fadi abubuwan da ya yi. To, idan ka samu dama mu yi adalci, mu kuma rike amana. Manzon Allah (s.a.w) ya ce, abu guda uku idan ka kauce su a cikin hadisi to, ka zama munafuki. Ka yi zance ka yo karya, a baka amana ka ci, a kuma amince maka ka yi yaudara.
Kuma sannan in na zo ga magoya baya su ma, su sani abubuwan da muke yi ba daidai bane, domin zagin shugabanni fasikanci ne, Annabi (s.a.w) ya fada.
Babu azzalumin shugaba irin wanda zai rika zalintar wadanda yake shugabanci. Haka kuma babu jahili mabiyi, wanda mabiyin da zai rika zagin shubanni. Wa ya fada maka zagi ake yi? ba zagi ake yi ba, saboda idan kana zagin shugabanninka sai ya zamar maka masifa. Ita masifa ko a’ina ba kaunarta ake yi ba, addu’a ake yi ko Allah ya gyara shi ko kuma Allah ya kawo maka madadinsa da zai maka adalci.
Ina fatan za mu yi amfani da koyi da Annabi (s.a.w), mu yi addu’a ga shugabanninmu ya kawo mana wadanda za su cece mu, ya basu dama su cece mu ko Allah ya shirye su. Amma idan muka ci gaba da zaginsu sai su zama lalatattu kuma a kanmu abun zai kare.
Allah ya sa mu dace.















Discussion about this post