Fadar Shugaban Ƙasa ta ƙaryata zargin cewa ana yunƙurin hana jam’iyyun adawa shiga babban zaɓen shekarar 2027, tana mai jaddada cewa fagen siyasar Nijeriya a buɗe yake ga kowa.
Mai bai wa Shugaban Ƙasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai da sadarwa, Sunday Dare, ya bayyana cewa babu wani shiri na takaita takardar zaɓe ga jam’iyyar mai mulki kaɗai wato APC.
- Sin Na Da Burin Ganin Al’ummun Sin Da Na Amurka Sun Ingiza Ruhin Diflomasiyar Kwallon Tebur
- ADC Ta Nuna Aniyar Kwace Borno A Shugabancin Ƙasa A 2027, Ta Soki Bola Tinubu
Dare, tsohon Ministan Matasa da Wasanni, ya yi wannan bayani ne a ranar Litinin yayin da yake magana a matsayin bako a shirin “Politics Today” na gidan talabijin na Channels.
Ya yi wannan bayani ne yayin da yake mayar da martani ga zanga-zangar da jam’iyyar ADC ta gudanar, kan matakin da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta ɗauka na dakatar da amincewa da tsagin shugabannin jam’iyyar, bisa umarnin kotu.
INEC ta dakatar da amincewa da shugabannin bangarorin ADC, ciki har da wanda David Mark ke jagoranta, tana mai cewa hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara da kuma rikice-rikicen cikin gida na jam’iyyar ne suka sa aka ɗauki wannan mataki.
Sai dai ADC ta bayyana wannan mataki a matsayin wani shiri na ƙoƙarin hana ta shiga zaɓen 2027, tare da gudanar da zanga-zanga domin nuna adawa da wannan hukunci.















Discussion about this post