Da Safiya yau Juma’a, babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta Sin Xi Jinping, ya gana da tawagar jam’iyyar Kuomintang ta Sin da shugabar jam’iyyar Cheng Li-wun ke jagoranta, a nan birnin Beijing.
Xi ya jaddada cewa, yana son hadin gwiwa da jam’iyyun siyasa na Taiwan da suka hada da jam’iyyar Kuomintang ta Sin da kungiyoyi da jama’a daga sassa daban-daban, don karfafa tattaunawa da musayar ra’ayi bisa ka’idar “kundin shaida matsaya daya da aka samu kan manufar ‘kasar Sin daya tak a duniya’ na 1992” da kuma adawa da “ware Taiwan daga kasar Sin”, domin samar da zaman lafiya ga bangarorin biyu da samar da jin dadi ga al’umma da kuma farfado da al’ummar kasar baki daya, tare da rike makomar dangantakar bangarorin biyu a hannun Sinawa da kansu.
Xi ya bayar da shawarwari guda hudu game da ci gaban dangantakar bangarorin biyu. Na farko, nacewa ga matsayar da ta dace don hadin gwiwar al’ummu tare. Na biyu, nacewa ga samun ci gaba lami lafiya don kiyaye kasar. Na uku, hadin kai da hadewa da juna don inganta jin dadin jama’a. Na hudu, tsayawa tsayin daka kan hadin kai da gwagwarmaya don cimma babban burin farfado da al’ummar Sinawa.
A nata bangaren, Cheng Li-wun ta bayyana cewa, ya kamata jam’iyyu biyu watau jam’iyyar kwaminis ta Sin da jam’iyyar Kuomintang ta Sin, su karfafa amincin siyasa, da taka rawar gani wajen zama dandalin tuntubar juna da himmatuwa wajen kiyaye tarihin kasar da yayata al’adunta, ta yadda za a samu ci gaba dangane da musayar ra’ayi da hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu a fannoni harkokin jama’a da jami’ai da kasuwanci da tattalin arziki, da al’adu, da sauransu. Haka zalika da tallafa wa ci gaban cudanyar matasa, don inganta jin dadin jama’a da ciyar da ci gaban dangantakar bangarorin biyu cikin zaman lafiya, da bude kyakkyawar makoma ga dangantakar bangarorin biyu, da kuma cimma babban burin farfado da al’ummar Sinawa baki daya. (Amina Xu)















Discussion about this post