A safiyar yau ranar 29 ga watan Yuni, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na Belarus Aleksandr Lukashenko a Diaoyutai a birnin Beijing.
Shugaba Xi ya nuna cewa, amincewar siyasa tsakanin Sin da Belarus tana da karfi kamar dutse, kuma an samu sakamako mai yawa wajen gina shawarar “ziri daya da hanya daya” a tsakaninsu, an kuma ciyar da manyan ayyukan hadin gwiwa gaba sosai, kana an kulla ingantaccen hadin gwiwa tsakanin mabambantan bangarori. Abun da ya tabbatar da cewa, zurfafa hadin gwiwar Sin da Belarus a kowane lokaci da kuma a dukkan fannoni ya dace da yanayin ci gaban al’ummun duniya, kuma ya dace da ainihin muradun al’ummomin kasashen biyu.
A nasa bangaren, Lukashenko ya bayyana cewa, ya yarda da maganar shugaba Xi game da dangantakar kasashen biyu gaba daya. Sin abokiyar hadin gwiwa ce ta dindindin ta Belarus a kowane lokaci, kuma hadin gwiwar bangarorin biyu yana da zurfi a dukkan fannoni, wanda ke ba da muhimmin goyon baya ga ci gaban tattalin arziki da zamantakewa na Belarus. (Amina Xu)














