Bisa ga ka’idojin kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta Sin wato JKS, membobin kwamitin siyasa na tsakiya na jam’iyyar, da sakatarorin sakatariyarta, da membobin majalisar wakilan jama’a ta kasar, da na majalisar zartarwa, da kuma membobin kwamitin JKS na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta jama’ar kasar Sin, da kotun jama’a ta koli ta kasar, da kuma sakatarorin kwamitin JKS na hukumar koli ta gabatar da kararraki ta jama’ar kasar Sin, a kwanan baya suka gabatar da rahoton aiki na shekara ta 2025 ga kwamitin tsakiyar JKS, da Xi Jinping, babban sakataren kwamitin tsakiya na jam’iyyar. Xi ya duba rahotannin aikin kuma ya ba da muhimmin umurni.
Xi ya jaddada cewa, a bana za a cika shekaru 105 da kafuwar jam’iyyar Kwaminis ta Sin, kuma ita ce shekarar farko da aiwatar da shirin ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al’ummar Sin na shekaru biyar-biyar karo na 15. Ya kamata a sauke nauyin dake wuya a cikin kowane aiki, a kuma yi aiki da himma tare da rike tsarin aiki na neman ci gaba cikin kwanciyar hankali, dole ne a aiwatar da sabon ra’ayin samun bunkasa a kowane bangare, da samun ingantaccen ci gaba a iyakacin kokari, kana da daidaita ci gaba da tsaro yadda ya kamata, da ci gaba da tabbatarwa da kuma inganta rayuwar jama’a, da kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin al’umma, ta yadda za a gaggauta tabbatar da farawar shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15 cikin wani yanayi mai armashi. (Amina Xu)














Discussion about this post