Hukumar siyasa ta kwamitin tsakiya na jam’iyyar kwaminis ta Sin ta yi karatu karo na 25, kan inganta karfin tinkarar bala’u daga indallahi a jiya Talata 28 ga wannan wata, inda babban sakataren kwamitin tsakiya na JKS Xi Jinping ya shugabanci karatun, tare da jaddada cewa ya kamata a gano muhimmancin ayyukan magancewa, da yaki da bala’u, da yin kokarin inganta karfin tinkarar bala’u don tabbatar da zaman rayuwa da dukiyoyin jama’a.
Xi Jinping ya kara da cewa, ya kamata a yi kokarin inganta fasahohi da dokokin dake shafar tinkarar bala’u daga indallahi, da sa kaimi ga dukkan jama’a da suke da karfin magancewa da yaki da bala’u, da kuma aiwatar da ayyukan magancewa da yaki da bala’u yadda ya kamata. (Zainab Zhang)















Discussion about this post