A yau Juma’a, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aike da sakon taya murna ga Ismail Omar Guelleh bisa sake lashe zaben shugaban kasar Djibouti.Xi Jinping ya ce dadaddiyar abota tsakanin Sin da Djibouti na da muhimmanci.
Yana cewa a shekarun baya-bayan nan, amincin bangarorin biyu a bangaren siyasa ya kara karfi, kuma hadin gwiwarsu ya haifar da kyawawan sakamako.
Ya kara da cewa, yana yaba wa da kudurin shugaba Guelleh na karfafa abota da hadin gwiwa tsakanin Sin da Djibouti a fannoni da dama. Kana yana daukar batun raya dangantakar kasashen biyu da matukar muhimmanci.
Bugu da kari, shugaba Xi ya ce a shirye ya ke ya ci gaba da hada hannu da shugaba Guelleh domin su ci gaba da goyon bayan juna kan batutuwan da suka shafe kasashen su da sauran manyan batutuwa da aiwatar da sakamakon taron dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afrika da ci gaba da bunkasa hadin gwiwar kasashen biyu bisa manyan tsare-tsare, domin jama’arsu su kara amfana da shi. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post