Yau 24 ga watan Afrilu, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aika da sakon taya murna ga Romuald Wadagni, bisa lashe zaben shugaban jamhuriyar Benin.Xi ya bayyana cewa, Sin da Benin suna da kyakkyawar alaka ta gargajiya.
Ya ce a ‘yan shekarun nan, bangarorin biyu sun ci gaba da zurfafa amincin siyasa a tsakaninsu da goyon bayan juna a kan muhimman batutuwan da suka shafi ainihin muradun kasashen biyu da manyan abubuwan da suke jan hankulansu.
Hadin gwiwarsu cikin zumunci a fannoni daban-daban ya samu babban ci gaba, wanda ya inganta jin dadin al’ummomin kasashen biyu.
Xi ya kara da cewa, yana darajanta ci gaban dangantakar Sin da Benin, kuma yana fatan hadin gwiwa da shugaba Wadagni, don ci gaba da aiwatar da sakamakon taron koli na dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC) da aka gudanar a birnin Beijing, da kuma ciyar da cikakkiyar dangantakar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Benin zuwa sabon matsayi. (Amina Xu)















Discussion about this post