Shugaban kasar Sin, Xi Jinping, ya aika da sakon taya murna ga Jami’ar Jilin wacce take bikin cika shekaru 80 da kafuwa a yau Laraba.
Xi ya mika sakon taya murna ga malamai, da dalibai, da kuma tsofaffin daliban jami’ar.Shugaba Xi ya jaddada fatan cewa, Jami’ar Jilin za ta yi amfani da cikakken karfinta a fannoni daban-daban wajen mayar da hankali kan muhimman bukatun kasa, da ci gaba da inganta tsarin fannonin karatu da kwarewa, da daga matsayin koyarwa da gudanar da bincike, da kara azamar yaye karin manyan kwararru masu hazaka, tare da bayar da gagarumar gudummawa wajen farfado da ci gaban yankin arewa maso gabashin kasar Sin a dukkan fannoni a sabon zamani, da kuma zurfafa cimma burin zamanantarwa ta kasar Sin. (Abdulrazaq Yahuza Jere)














