An kaddamar da taron ministocin kasuwanci na kasashe membobin kungiyar APEC a birnin Suzhou na lardin Jiangsu da ke gabashin kasar Sin jiya Jumma’a 22 ga watan nan. Tuni a ranar Alhamis, aka bude taron tattaunawa na inganta abotar bangarorin masana’antu da kasuwanci na yankin Asiya da tekun Pasifik, wanda kuma shi ne babban taron jawo hankalin ’yan kasuwan sassan kasa da kasa na Suzhou na shekarar 2026, inda ya samu halartar wakilan kamfanoni sama da 700 daga kasashe da yankuna fiye da 30.
Mahalartan na sa ran amfani da damarmakin “shekarar kasar Sin” yayin taron APEC, don fadada hadin gwiwar tattalin arziki da kasuwanci.
A yayin babban taron na wannan karo, baki daga kamfanonin Amurka sun fi yawa. Kuma sabon binciken da kungiyar ’yan kasuwan Amurka a kasar Sin ta yi, ya nuna cewa, kaso 60 bisa dari na kamfanonin Amurka na shirin habaka zuba jari a Sin.
Da yake tsokaci, shugaban kungiyar ’yan kasuwan Amurka da ke birnin Shanghai, Eric Zheng ya ce, “muna sa ran halartar taron ministocin kasuwanci na kasashe membobin kungiyar APEC na bana a Suzhou, kuma muna fatan taron zai shirya tunkarar abubuwan da za su taso a nan gaba, da lalubo bakin zaren daidaita kalubalen da duniya take fuskanta, ciki har da tattalin arziki na dijital, da raya tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba, da ingancin tsarin samar da kayayyaki da sauransu. Muna kuma fatan taron zai kara jagorantar kamfanonin waje, ciki har da na Amurka, wajen zuba jari a Suzhou.” (Murtala Zhang)















Discussion about this post