ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ake Kula Da Jama’a Ya Fi Muhimmanci

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Jama'a

Jaridar “The Nation” da ake wallafawa a Najeriya, ta wallafa wani bayani mai ban sha’awa a kwanan baya, mai taken ”Bayan aiki mai inganci na kwashe ‘yan kasa da kasar Sin ta yi”, wanda ya ce, bayan tsanantar yanayin yakin da ake yi tsakanin Isra’ila da Lebanon, gwamnatin kasar Sin ta kwashe ‘yan kasar fiye da 200 daga kasar Lebanon cikin wasu kwanaki 2 zuwa 3, har da iyalansu ‘yan wasu kasashe daban daban. Kana sabanin ingantaccen matakin da kasar Sin ta dauka, kasar Amurka, da ta kan soki sauran kasashe, ta fakewa da batun ”kare dimokuradiyya da ‘yancin dan Adam”, ta ki daukar matakin janye Amurkawa daga Lebanon, inda a maimakon haka, ta bukaci Amurkawan dake Lebanon da su sayi tikitin jirgi da kansu don barin kasar. Wannan yanayi na ko-in-kula da gwamnatin kasar Amurka ta nuna ya bakanta ran dimbin ‘yan kasar, har ma sun rubuta a shafin yanar gizo mai dauke da labarin, cewa ”Kamar bai ishe su ba su yi amfani da kudin jama’a wajen kashe ‘yan kasar Lenanon, yanzu ko ‘yan kasar Amurka ma za su fara kashewa.” 

 

Sa’an nan an bayyana a cikin wannan bayani cewa, ta hanyar kwatantawa, za a iya ganin yadda kasar Sin ke kokarin sauke nauyin dake bisa wuyanta, gami da karfin kasar na kubutar da ‘ya’yanta da abokanta daga yanayi mai cike da hadari.

ADVERTISEMENT
  • Magoya Baya Sun Kori Kwankwaso Daga NNPP, Sun Kona Jar Hula A Jihar Neja
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Kafa Kwamitin Da Zai Fara Sayar Da Kayan Abinci Masu Sauki

Hakika, idan mun kwatanta sakamakon da aka samu a kasar Sin da na Amurka, ta fuskar tinkarar dimbin abubuwan da suka auku ba zato ba tsammani, za mu iya ganin yadda ake samun bambanci sosai tsakanin kasashen 2. Misali, tun daga watan Satumba har zuwa farkon watan da muke ciki, dukkanin kasashen 2 wato Sin da Amurka sun taba fuskantar mahaukaciyar guguwa guda 2. Kana a cikinsu wata guguwar da ta aukawa babban yankin kasar Sin ta fi sauran 3 karfi. Amma a karshe an samu daruruwan mutanen da suka rasa rayuka a kasar Amurka sakamakon bala’in guguwa, yayin da adadin bangaren Sin mutum 6 ne kacal.

 

LABARAI MASU NASABA

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

To ko me ya sa ake samun wannan babban bambanci? Hakika kasar Sin ta shirya sosai kafin zuwan guguwar, inda aka rufe makarantu da wuraren yawon shakatawa cikin gaggawa, da kwashe mutane fiye da dubu dari daya zuwa sauran wurare, da shirya kayayyakin da ake bukata wajen tinkarar bala’i, gami da sanya sojoji su kimtsa don gudanar da aikin ceto daga bisani. Sa’an nan bayan da bala’in guguwa ya auku, sojoji da ‘yan kwana-kwana, da fararen hula sun yi hadin gwiwa a kokacin maido da hidimomin samar da ruwa, da wutar lantarki, da sadarwa, cikin sauri. Bayan wasu kwanaki, an kai ga gyara yawancin kayayyakin more rayuwa da suka lalace.

 

Sa’an nan a kasar Amurka, abun da ya faru shi ne, ba a kimtsa sosai tun kafin aukuwar bala’in ba. A cewar Zhou Deyu, wani masanin ilimin harkar siyasa, da ya samu digiri na 3 a jami’ar Pittsburgh ta kasar Amurka, ba a son daukar matakan kandagarkin bala’i a kasar Amurka, saboda yin haka zai janyo suka daga ‘yan siyasa abokan gaba, su rika cewa wai ana rigakafi fiye da kima, da salwantar da kudin jama’a. Ban da haka, ‘yan siyasan kasar na son zuba kudi bayan aukuwar bala’i, ta yadda jama’a za su yi musu matukar godiya, maimakon kare jama’a daga tasirin bala’i tun da farko. Sa’an nan, yadda ba a kimtsa sosai tun kafin abkuwar bala’i ba, ya haddasa karancin kudin da ake bukata don gudanar da aikin ceto da ba da tallafi, bayan da bala’in ya auku.

 

An ce kusan wasu makonni 2 bayan aukuwar bala’in guguwa, gwamnatin Amurka ta samar da dala miliyan 30 da wani abu don gudanar da aikin ceto. Yayin da a dayan bangare, a ranar da bala’in guguwa ya auku kadai, kasar Isra’ila ta tabbatar da damar samun tallafin aikin soja na dala biliyan 8.7 daga kasar Amurka.

 

Idan an yi bincike kan dalili na tushe, wanda ya sa ake samun bambancin tsakanin kasar Sin da kasar Amurka a fannin kula da wasu batutuwan da suka abku ba zato ba tsammani, to, za a ga ya shafi tunanin masu gudanar da mulki na kasashen 2. A kasar Sin, daya daga cikin tunanin mulki masu muhimmanci na gwamnatin kasar shi ne mai da moriyar jama’a gaban komai, da kokarin bautawa jama’a. Wannan tunani ya sa kasar yin iyakacin kokarin kare rayuka da dukiyoyin jama’a yayin da ake fuskantar bala’i, da tallafawa marasa karfi, da kokarin kawar da talauci bayan yanayin tattalin arzikin kasar ya inganta, gami da neman raya bangarorin horaswa, da rage talauci, da samar da guraben aikin yi, yayin da take hadin gwiwa tare da kasashen Afirka, don sanya zamanantarwar nahiyar Afirka amfanin al’ummunta. Kana a nata bangare, manyan kusoshi masu ikon mulki na kasar Amurka, sun fi dora muhimmanci kan moriya a fannin siyasa. Misali, ginshikin mamban jam’iyyar Republican ta kasar Amurka Lindsey Graham, ya fada wa kafofin watsa labarun kasar cewa, idan an kwatanta da aikin ceton jama’ar kasarsa da bala’in guguwa ya ritsa da su, aikin tallafawa kasar Isra’ila don ta ci gaba da gudanar da yake-yake ya fi muhimmanci.

 

A cikin bayanin da jaridar the Nation ta wallafa, editanta ya mai da hankali kan karfin da wata kasa ta nuna, ta hanyar gudanar da aikin kwashe ‘ya’yanta daga sauran kasashe. Sai dai a gani na, wani abun da ya fi muhimmanci, da dacewa da lura, shi ne yadda wata kasa ke kula da ‘ya’yanta. Saboda idan wata kasa ba ta taba dora muhimmanci kan rayukan jama’arta ba, to, ta yaya za ta kula da jama’ar sauran kasashe? (Bello Wang)

Jama'a
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa
Jama'a
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi
  • Sulaiman
    Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC
  • Sulaiman
    Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

MASU ALAKA

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin

July 1, 2026
Next Post
Jirgin Ƙasa Na ‘Red Line’ Ya Fara Aiki Yau A Legas 

Jirgin Ƙasa Na 'Red Line' Ya Fara Aiki Yau A Legas 

LABARAI MASU NASABA

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.