ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ake Zama Da Uwar Miji  (2)

by Bilkisu Tijjani
6 months ago
Miji

5)- Ki riƙa kwaɗaitar da mijinki a kan ya riƙa ziyartar su ko da kuwa a gari ɗaya suke.

Sannan ki riƙa kwaɗaitar da shi akan ɗaukan ki da ƴaƴanki ku je ku wuni mata, kin ga za ta ji daɗi, kuma ki kwaɓi ƴaƴanki kafin ku je, domin kada su yi ta mata dambe da rashin kunya da barna, su sa ta ji haushin ki ta ce baki ba ma jikokinta tarbiyya ba.

Sannan duk ƙawayen uwar mijinki ki riƙa girmama su suma, kuma ki riƙa musu kyauta daga lokaci zuwa lokaci, hikimar yin haka ita ce duk abin da ki ka ba su za su ba ta labari, kin ga za ta ji daɗi ta ƙara sonki.

ADVERTISEMENT

Idan mijinki zai saya wa mahaifiyarsa zani, to kada ki yi mugunta, ke ki sa mai tsada ita kuma ki ce a saya mata mai araha wanda ba zai kai ko ina ba zai koɗe, idan ya saya miki mai kyau ita ma ki ce ya saya mata mai kyau.

  • Ɓata-gari Sun Kashe Matar Aure Da ’Ya’yanta 3 A Kano
  • Muhimmancin Koya Wa ‘Yan Mata Ayyukan Gida Kafin Shiga Gidan Miji

Ki riƙa tunatar da shi wurin saya musu kayan abinci, da yi musu sutura akai-akai, domin da ban tausayi ka ga namiji gidansa ana cin kaji amma miyar mahaifiyarsa kamar ruwan wanke kai. Wallahi sai Allah ya saka mata, idan ya sayo kaji goma ko bai ce ba, ki ce wane zan cire biyu in yi wa Inna miya mu je a kai mata, kuma shi ma zai ƙara sonki.

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Sannan ko da wasa ka da ki sake ki riƙa zagin uwar mijinki, domin wallahi magana fa tana zagayawa, za ki yi mamakin jin maganganun banzan da kika yi ya kai kunnenta, babu ruwan ki, ko da ki na kyautata mata amma ba ta sonki ki ci gaba wata rana za ta soki, idan har kina kyautata mata.

Sannan idan kin je yi mata wuni, to fa kada ki zauna baki komai, ɗaki ya yi datti amma kin ƙi gyarawa, in ma son samu ne kina zuwa ki fara mata hidima, ki kwaso kayanta ki wanke, ki share ciki da wajen ɗakin, ki mata goge-goge, wata ma idan ta iya kitso har tsefe kan uwar mijinta take yi, ta wanke mata ta rangaɗa mata kitso, ko kuma ta ce a kira mai kitso ta biya kuɗin a yi mata.

Wannan duka muna ɗaukar su abin wasa, amma ba haka bane, rashin kula da su shi ya sa iyayen mazajenmu suke takura mana, suke tsanar mu, kuma wani lokacin suna da gaskiya, domin waɗansu suna daina zawa gaishe da iyayensu tun daga lokacin da suka yi aure, ke kuma baki iya kwaɗaitar da shi ba. Wannan shi zai saka ta fara cewa ke ce kike hana shi.

Waɗansu matan ma har zagin uwar miji suke yi duk inda kika zauna sai ka zagye ta, idan za ai mata zani mai tsada ki hana, baki zuwa gaishe ta, kin je mata wuni kina cika kina batsewa dole ta tsaneki. Suma ƴan’uwansa dole su tsane ki domin mahaifiyarsa ba ta sonki.

Ƴan uwa mata sai mu ɗauki darasi domin mu san irin dubarun da zamu zauna da uwar miji da kyau.

Miji
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji

MASU ALAKA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
Next Post
Haɗin Gyaran Mace

Haɗin Gyaran Mace

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.