ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

by Bilkisu Tijjani and Sulaiman
2 months ago
Uwargida

Kishi wani yanayi ne da ke tasowa a zuciyar mutum sakamakon cakuɗuwar fushi, hassada, ƙyashi da ƙin yarda da shiga cikin abin da yake ganin nasa ne. Wannan yanayi kan bayyana ne idan mutum ya ji cewa wani yana son shiga huruminsa ko kuma ya yi tarayya da shi a abin da yake so ko ya mallaka.

Manzon Allah Sallalahu Alaihi Wasallam ya sanar da mu cewa Allah Maɗaukakin Sarki yana da kishin da ya dace da Shi, haka kuma ya halicci bayinsa da kishi a cikin ɗabi’unsu. Sai dai Allah shi ne mafificin masu kishi.

Kishi ya kasu gida biyu:

ADVERTISEMENT

1. Kishi mai kyau:

Kishi mai kyau shi ne wanda mutum yake iya sarrafa zuciyarsa da kuma hana ta bin son rai. A lokacin da hassada, ƙeta ko ƙyashi suka taso, sai yayi ƙoƙarin danne su, maimakon ya bari su rinjaye shi. Irin wannan kishi kan sa mutum ya yi burin samun irin alherin da wani yake da shi ba tare da ya yi masa hassada ko ya yi fatan ya rasa abin ba. Haka kuma yana taimaka wa mutum ya kula da abin da yake so ba tare da son mallake shi shi kaɗai ba, musamman idan abin yana da masu tarayya da shi, kamar miji a tsarin aure. Manzon Allah Sallalahu Alaihi Wasallam ya ce:

LABARAI MASU NASABA

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

“Imanin ɗayanku ba zai cika ba har sai ya so wa ɗan’uwansa abin da yake so wa kansa.”

Kishi marar kyau:

Kishi marar kyau kuwa shi ne wanda hassada, ƙeta da ƙyashi suka mamaye zuciya har mutum ya kasa sarrafa kansa. Wannan ne ke haifar da zafin kishi wanda wani lokaci kan kai ga aikata munanan ɗabi’u da ayyuka. A wannan rubutu, za mu yi bayani ne kan wasu daga cikin abubuwan da ke haddasa zafin kishi a cikin al’umma.

Dalilan da ke haddasa zafin kishi:

1. Rashin kyakkyawar tarbiyya tun Ƙuruciya:

Wasu lokuta matsalar zafin kishi ta samo asali ne daga irin tarbiyyar da yarinya ta samu tun tana ƙarama. Akwai iyaye mata da ke cusa wa ‘yaƴansu tun suna yara cewa kishiya abokiyar gaba ce, suna kuma nuna musu hakan ta hanyar munanan kalamai ko mummunar mu’amala da abokan zamansu. Idan irin wannan tunani ya ginu a zuciyar yarinya tun tana ƙarama, ilimin boko ko na addini kaɗai ba zai wadatar wajen kawar da shi ba matuƙar ba a gyara tushen matsalar ba.

2. Rashin haɗa Ilimi da Tarbiyya

A wasu makarantu ana mayar da hankali ne kan koyar da ilimi kawai, ba tare da ba da muhimmanci ga tarbiyya ba. Wannan ne ya sa wani lokaci mutum zai kasance mai ilimi amma ba shi da kyawawan ɗabi’u. A da, malamai suna haɗa ilimi da tarbiyya, abin da ya taimaka wajen gina mutanen kirki a cikin al’umma.

3. Wasu kurakuran mazaje:

Wasu mazan kan yi alkawurran da ba su da tabbacin cika su, musamman kafin aure. Wasu kan yi wa mace alkawarin cewa ba za su ƙara aure ba, sannan daga baya su canja ra’ayi.

Irin wannan yanayi kan haifar da rashin jituwa da fitina a gida, musamman idan an gina aure ne a kan abin da ba zai yiwu a tabbatar da shi ba.

4. Rashin Adalci Tsakanin Mata:

Rashin adalci tsakanin mata na daga cikin manyan abubuwan da ke haddasa fitina a gidajen aure. Idan mace ta ji ana nuna son kai ko ana tauye mata hakkinta, hakan kan haddasa ɓacin rai da rikice-rikice.

Uwargida
Bilkisu Tijjani
+ posts Bio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Tuwon Alkama Da Miyar Taushe
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Kula Da Labba Domin Su Kasance Masu Laushi
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Chicken Teriyaki Rice
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Kare Hannu Daga Bushewa
Uwargida
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)
Uwargida Sarautar Mata

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

July 5, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)
Uwargida Sarautar Mata

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026
Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa
Uwargida Sarautar Mata

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa

May 30, 2026
Next Post
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.