Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa ya kai ziyarar duba aiki a sabuwar cibiyar gyaran motoci mai amfani da hasken rana da iskar gas na zamani, domin kula da gyare-gyaren motocin da gwamnatin jihar ta sawo kwanakin baya.
Idan za a iya tunawa dai, gwmanatin jihar ta amince da sawo motocin guda 30 a zamanta na majalisar zartaswa karo na 14 wanda ya gudana a shekarar da ta gabata.
Gwamna Malam Raɗɗa wanda Malam Ibrahim Bello ya zagaya da shi a cikin cibiyar sun duba dukkan wuraren da ake haɗa kayan motocin na ciki da na waje har ya zuwa matakin kammala haɗa motocin a fara aiki da su.
An kafa cibiyar ne domin kula da gyaran irin waɗanna ababen hawan na zamani ƙarƙashin shirin inganta harkokin sufuri a jihar.
Waɗannan motoci za su taka muhimmiyar rawa wajen ƙoƙarin inganta harkokin sufuri ga ɗalibai, hada-hadar yau da kullum, tare da sauran al’ummomin gari da ke a ko’ina a faɗin jihar.
Haka nan kuma cibiyar za ta taimaka masu saka hannun jari mai tsawon lokaci dangane da shirin samar da motocin masu amfani da hasken rana da iskar gas na zamani.














