ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamna Lawal Ya Samu Gagarumar Tarba A Ɗansadau

by Sulaiman
7 months ago
Gwamna lawal

Dubban jama’a ne suka mamaye manyan ƙauyuka da hanyoyin da ke kaiwa garin Ɗansadau domin tarbar Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, a wata ziyara ta tarihi da ya kai yankin.

A ranar Laraba ne gwamnan ya ziyarci al’ummar Ɗansadau da ke Ƙaramar Hukumar Maru, ziyara da ta ɗauki hankalin jama’a tare da nuna farin cikin al’umma bisa zuwansa.

  • Kifi Na Ganin Ka Mai Jar Koma!
  • Tinubu Zai Gabatar Da Daftarin Kasafin Kuɗin 2026 Ga Majalisun Tarayya

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa kusan shekaru fiye da ashirin kenan rabon da wani gwamnan Zamfara ya taka ƙafa zuwa Dansadau, tun daga zamanin tsohon gwamna Ahmad Sani Yariman Bakura.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ƙara da cewa, Dansadau, wadda ita ce mafi girman gunduma a Ƙaramar Hukumar Maru, ta shafe tsawon lokaci cikin mantuwa da sakaci daga gwamnatocin baya, duk da girman al’ummarta da muhimmancinta ga ci gaban yankin.

A yayin ziyarar, Gwamna Lawal ya ratsa wasu al’ummomi da suka haɗa da Wanke, Magami da Dan Gulbi, inda jama’a suka fito kwansu da kwarkwata domin nuna masa ƙauna da goyon baya.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

Gwamnan ya kuma duba aikin gina titin Gusau zuwa Dansadau mai tsawon kilomita 108, wanda gwamnatinsa ta bayar da kwangilar aiwatarwa a matsayin wani muhimmin bangare na ƙoƙarin buɗe hanyoyin sufuri da bunƙasa tattalin arzikin yankin.

A wani bangare na ziyarar, Sarkin Dansadau, Mai Martaba Alhaji Garba Mohammed Sarkin Kudu, ya karrama Gwamna Lawal da sarautar gargajiya ta Garkuwan Dansadau, a matsayin girmamawa ga yadda ya nuna damuwa da sha’awar kawo ci gaba ga yankin.

Masu lura da al’amuran siyasa na ganin cewa wannan ziyara ta nuna ƙarara ƙudurin Gwamna Lawal na sauka ƙasa-ƙasa domin kusantar al’umma da kuma tabbatar da cewa ayyukan raya ƙasa sun shafi dukkan sassan jihar. Tarbar da jama’ar Dansadau suka yi masa na nuni da ƙaruwar goyon bayan da gwamnatinsa ke samu, sakamakon manyan shirye-shiryen raya ƙasa da ake aiwatarwa ƙarƙashin manufar ‘Zamfara Rescue Mission’.

A cewar jama’a, ziyarar gwamnan ta sake farfaɗo da fata da kwarin gwiwa cewa Dansadau da makamantanta ba za su sake zama a bayan layi ba a tsarin ci gaban jihar Zamfara.

Gwamna lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani
  • Sulaiman
    Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana
  • Sulaiman
    Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?
  • Sulaiman
    Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160
Manyan Labarai

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Next Post
Jan Aikin Da Ke Gaban Sabon Babban Ministan Tsaro

Jan Aikin Da Ke Gaban Sabon Babban Ministan Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026
Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark

Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark

July 13, 2026
Majalisar Gudanarwa Ta Sin Ta Wallafa “Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Karo Na 15 Kan Kiyaye Lafiyar Al’ummar Kasar”

Majalisar Gudanarwa Ta Sin Ta Wallafa “Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Karo Na 15 Kan Kiyaye Lafiyar Al’ummar Kasar”

July 13, 2026
Xi Zai Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026, Inda Zai Gabatar Da Muhimmin Jawabi

Xi Zai Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026, Inda Zai Gabatar Da Muhimmin Jawabi

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.