ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamna Lawal Ya Samu Gagarumar Tarba A Ɗansadau

by Sulaiman
6 months ago
Gwamna lawal

Dubban jama’a ne suka mamaye manyan ƙauyuka da hanyoyin da ke kaiwa garin Ɗansadau domin tarbar Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, a wata ziyara ta tarihi da ya kai yankin.

A ranar Laraba ne gwamnan ya ziyarci al’ummar Ɗansadau da ke Ƙaramar Hukumar Maru, ziyara da ta ɗauki hankalin jama’a tare da nuna farin cikin al’umma bisa zuwansa.

  • Kifi Na Ganin Ka Mai Jar Koma!
  • Tinubu Zai Gabatar Da Daftarin Kasafin Kuɗin 2026 Ga Majalisun Tarayya

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa kusan shekaru fiye da ashirin kenan rabon da wani gwamnan Zamfara ya taka ƙafa zuwa Dansadau, tun daga zamanin tsohon gwamna Ahmad Sani Yariman Bakura.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ƙara da cewa, Dansadau, wadda ita ce mafi girman gunduma a Ƙaramar Hukumar Maru, ta shafe tsawon lokaci cikin mantuwa da sakaci daga gwamnatocin baya, duk da girman al’ummarta da muhimmancinta ga ci gaban yankin.

A yayin ziyarar, Gwamna Lawal ya ratsa wasu al’ummomi da suka haɗa da Wanke, Magami da Dan Gulbi, inda jama’a suka fito kwansu da kwarkwata domin nuna masa ƙauna da goyon baya.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnan ya kuma duba aikin gina titin Gusau zuwa Dansadau mai tsawon kilomita 108, wanda gwamnatinsa ta bayar da kwangilar aiwatarwa a matsayin wani muhimmin bangare na ƙoƙarin buɗe hanyoyin sufuri da bunƙasa tattalin arzikin yankin.

A wani bangare na ziyarar, Sarkin Dansadau, Mai Martaba Alhaji Garba Mohammed Sarkin Kudu, ya karrama Gwamna Lawal da sarautar gargajiya ta Garkuwan Dansadau, a matsayin girmamawa ga yadda ya nuna damuwa da sha’awar kawo ci gaba ga yankin.

Masu lura da al’amuran siyasa na ganin cewa wannan ziyara ta nuna ƙarara ƙudurin Gwamna Lawal na sauka ƙasa-ƙasa domin kusantar al’umma da kuma tabbatar da cewa ayyukan raya ƙasa sun shafi dukkan sassan jihar. Tarbar da jama’ar Dansadau suka yi masa na nuni da ƙaruwar goyon bayan da gwamnatinsa ke samu, sakamakon manyan shirye-shiryen raya ƙasa da ake aiwatarwa ƙarƙashin manufar ‘Zamfara Rescue Mission’.

A cewar jama’a, ziyarar gwamnan ta sake farfaɗo da fata da kwarin gwiwa cewa Dansadau da makamantanta ba za su sake zama a bayan layi ba a tsarin ci gaban jihar Zamfara.

Gwamna lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Jan Aikin Da Ke Gaban Sabon Babban Ministan Tsaro

Jan Aikin Da Ke Gaban Sabon Babban Ministan Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.