• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jam’iyyar NNPP Ta Rasa Kujeru 3 Na Majalisar Wakilai A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
in Labarai
0
NNPP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanzu haka kotun sauraron korafe-korafen zabe da ke zamanta a Jihar Kano ta mayar wa da Jam’iyyar APC kujeru uku daga cikin kujerun da ta kalubalantar Jam’iyyar NNPP mai mulki da mallakarsu tun da farko.

Shara’ar zabe dai a Kano ta fara daukar sabon yanayi, inda tun a cikin makon da ya gabata kotun ta karbe kujerar wakilin karamar Hukumar Tarauni, wanda a farko aka ayyana Jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ta lashe zaben. Sai dai sakamako bai yi wa Jam’iyyar APC dadi ba, dan takararta Honarabul Hafizu Ibrahim Kawu ya garzaya gaban kotu, inda ya kalubalanci rashin sahihancin sunan da dan takarar Jam’iyyar NNPP ke amfani da shi. Sakamakon wannan korafin, bayan sauraron bangarorin biyu, kotun ta yanke hukuncin mayarwa da Honarabul Hafizu Kawu wannan kujera.

  • Kotun Zaben Gwamnan Taraba: Cikin Matsi INEC Ta Ayyana Sakamako, A Sake Bitar Zaben – NNPP

Haka zalika, kotun ta sake karbe kujerar wakilin kananan Hukumomin Kura, Madobi da Garun Malam, wadda dan Jam’iyyar NNPP aka bayyana a matsayin wanda ya lashe zaben. Wanda ya yi wa Jam’iyyar APC takara, Honarabul Musa Iliyasu Kwankwaso ya garzaya kotu, inda ya zargi cewa dan takarar NNPP bai aje aikinsa ba kamar yadda dokokin hukumar zabe suka gindaya. Hakan ya sa kotun duba hujjojin da lauyoyin bangaren masu korafi suka gabatar, sannan kuma ta yanke hukuncin mayar wa Musa Iliyasu Kwnakwaso na Jam’iyyar APC a matsayin halastacen wanda ya lashe zaben.

Ita ma kujerar karamar Hukumar Kumbotso wadda tun farko aka ayyna Honarabul Idris Dan Kawu a matsayin wanda ya lashe zaben. Kotun sauraron korafe-korafen zaben ta kwace wannan nasara, inda ta tabbatar wa Honarabul Manniru Babba Dan Agundi a matsayin wanda ya lashe zaben tare da cin tarar Idris Dan Kawu naira 200,000.00 ko zaman gidan gyaran hali na watanni shida.

Zuwa yanzu jam’iyyar adawa ta APC ta samu nasarar karbe kujeru uku daga cikin kujerun da suke kalubalantar jam’iyyar NNPP kan ikirarin lashe zabensu, yanzu dai ko shakka babu kallo ya r koma sama, domin bisa ga dukkan alamu wankin hula na neman kai jam’iyya mai mulki ta NNPP dare, ta yadda ake masu dauki dai-dai a kujerun da suke ikirarin lashewa. Wanda kuma har yanzu akwai sauran wasu masu yawa da suke gaban kotu da jam’iyyar APC ke kalubalantar nasararsu.

Labarai Masu Nasaba

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

Wanann hali da jam’iyyar NNPP ta tsinci kai a ciki ya sa wasu magoya bayanta fara sun tunanin me jagororin jam’iyyar NNPP ke ciki zuwa yanzu da suka zuba ido ana ta yi masu dauki dai-dai. Sannan wasu na ganin daman ‘yan takarkarun na Jam’iyyar ta NNPP ba a yi masu taza da tsifa ba kafin tsaryar da su takarar. Wannan ta sa a ganin wasu suke zargin daman ba mamaki an yi kitso da kwarkwata. Baya ga wannan ita Jam’iyyar NNPP daman a Jihar Kano kadai take da adadin kujerun da suke tinkaho da su kuma wasu na ganin takun sakar da jagoran darikar ta Kwankwasiyya, Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso ke yi da wasu shugabanni masu rike da madafun iko ya kara haifar wa da jam’iyyar tarnaki.

Yanzu dai masu fashin baki na ganin wannan karbe kujerun da jam’iyyar adawa ta APC ke yi na zaman wata ‘yar manuniya da ke haska hukuncin kotun da ake sauraron shari’ar da ake yi tsakanin Gwamna Abba Kabir Yusuf da kuma Dakta Nasiru Yusuf Gawuna na jam’iyyar APC, wanda a iya cewa ba a san maci tuwo ba sai miya ta kare.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: kanoKwankwasiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Babbar Darektar UNEP Ta Nuna Yabo Ga Matakan Kasar Sin Na Kiyaye Muhallin Halittu

Next Post

Sin Na Bin Diddigin Hasarar Rayuka Da Dukiyoyi Da Mahaukaciyar Guguwa Ta Haddasa A Gabashin Libya

Related

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC
Labarai

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

9 hours ago
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
Da ɗumi-ɗuminsa

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

10 hours ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Da ɗumi-ɗuminsa

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

11 hours ago
Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar

12 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Da ɗumi-ɗuminsa

Lauyoyin Majalisar Dattawa Sun Ƙaryata Natasha Kan Cewa Kotu Ta Ce Ta Koma Bakin Aiki

14 hours ago
Namadi Sambo Ya Yaba Wa Gwamna Abba Yusuf Kan Bunƙasa Ɓangaren Ilimi Da Gine-Gine A Kano
Manyan Labarai

Namadi Sambo Ya Yaba Wa Gwamna Abba Yusuf Kan Bunƙasa Ɓangaren Ilimi Da Gine-Gine A Kano

15 hours ago
Next Post
Libya

Sin Na Bin Diddigin Hasarar Rayuka Da Dukiyoyi Da Mahaukaciyar Guguwa Ta Haddasa A Gabashin Libya

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

July 7, 2025
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

July 7, 2025
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

July 7, 2025
Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan

Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.