ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jam’iyyar NNPP Ta Rasa Kujeru 3 Na Majalisar Wakilai A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
NNPP

Yanzu haka kotun sauraron korafe-korafen zabe da ke zamanta a Jihar Kano ta mayar wa da Jam’iyyar APC kujeru uku daga cikin kujerun da ta kalubalantar Jam’iyyar NNPP mai mulki da mallakarsu tun da farko.

Shara’ar zabe dai a Kano ta fara daukar sabon yanayi, inda tun a cikin makon da ya gabata kotun ta karbe kujerar wakilin karamar Hukumar Tarauni, wanda a farko aka ayyana Jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ta lashe zaben. Sai dai sakamako bai yi wa Jam’iyyar APC dadi ba, dan takararta Honarabul Hafizu Ibrahim Kawu ya garzaya gaban kotu, inda ya kalubalanci rashin sahihancin sunan da dan takarar Jam’iyyar NNPP ke amfani da shi. Sakamakon wannan korafin, bayan sauraron bangarorin biyu, kotun ta yanke hukuncin mayarwa da Honarabul Hafizu Kawu wannan kujera.

  • Kotun Zaben Gwamnan Taraba: Cikin Matsi INEC Ta Ayyana Sakamako, A Sake Bitar Zaben – NNPP

Haka zalika, kotun ta sake karbe kujerar wakilin kananan Hukumomin Kura, Madobi da Garun Malam, wadda dan Jam’iyyar NNPP aka bayyana a matsayin wanda ya lashe zaben. Wanda ya yi wa Jam’iyyar APC takara, Honarabul Musa Iliyasu Kwankwaso ya garzaya kotu, inda ya zargi cewa dan takarar NNPP bai aje aikinsa ba kamar yadda dokokin hukumar zabe suka gindaya. Hakan ya sa kotun duba hujjojin da lauyoyin bangaren masu korafi suka gabatar, sannan kuma ta yanke hukuncin mayar wa Musa Iliyasu Kwnakwaso na Jam’iyyar APC a matsayin halastacen wanda ya lashe zaben.

ADVERTISEMENT

Ita ma kujerar karamar Hukumar Kumbotso wadda tun farko aka ayyna Honarabul Idris Dan Kawu a matsayin wanda ya lashe zaben. Kotun sauraron korafe-korafen zaben ta kwace wannan nasara, inda ta tabbatar wa Honarabul Manniru Babba Dan Agundi a matsayin wanda ya lashe zaben tare da cin tarar Idris Dan Kawu naira 200,000.00 ko zaman gidan gyaran hali na watanni shida.

Zuwa yanzu jam’iyyar adawa ta APC ta samu nasarar karbe kujeru uku daga cikin kujerun da suke kalubalantar jam’iyyar NNPP kan ikirarin lashe zabensu, yanzu dai ko shakka babu kallo ya r koma sama, domin bisa ga dukkan alamu wankin hula na neman kai jam’iyya mai mulki ta NNPP dare, ta yadda ake masu dauki dai-dai a kujerun da suke ikirarin lashewa. Wanda kuma har yanzu akwai sauran wasu masu yawa da suke gaban kotu da jam’iyyar APC ke kalubalantar nasararsu.

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

Wanann hali da jam’iyyar NNPP ta tsinci kai a ciki ya sa wasu magoya bayanta fara sun tunanin me jagororin jam’iyyar NNPP ke ciki zuwa yanzu da suka zuba ido ana ta yi masu dauki dai-dai. Sannan wasu na ganin daman ‘yan takarkarun na Jam’iyyar ta NNPP ba a yi masu taza da tsifa ba kafin tsaryar da su takarar. Wannan ta sa a ganin wasu suke zargin daman ba mamaki an yi kitso da kwarkwata. Baya ga wannan ita Jam’iyyar NNPP daman a Jihar Kano kadai take da adadin kujerun da suke tinkaho da su kuma wasu na ganin takun sakar da jagoran darikar ta Kwankwasiyya, Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso ke yi da wasu shugabanni masu rike da madafun iko ya kara haifar wa da jam’iyyar tarnaki.

Yanzu dai masu fashin baki na ganin wannan karbe kujerun da jam’iyyar adawa ta APC ke yi na zaman wata ‘yar manuniya da ke haska hukuncin kotun da ake sauraron shari’ar da ake yi tsakanin Gwamna Abba Kabir Yusuf da kuma Dakta Nasiru Yusuf Gawuna na jam’iyyar APC, wanda a iya cewa ba a san maci tuwo ba sai miya ta kare.

 

NNPP
Abdullahi Muh'd Sheka
+ postsBio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
Libya

Sin Na Bin Diddigin Hasarar Rayuka Da Dukiyoyi Da Mahaukaciyar Guguwa Ta Haddasa A Gabashin Libya

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.