• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jam’iyyar NNPP Ta Rasa Kujeru 3 Na Majalisar Wakilai A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
in Labarai
0
NNPP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanzu haka kotun sauraron korafe-korafen zabe da ke zamanta a Jihar Kano ta mayar wa da Jam’iyyar APC kujeru uku daga cikin kujerun da ta kalubalantar Jam’iyyar NNPP mai mulki da mallakarsu tun da farko.

Shara’ar zabe dai a Kano ta fara daukar sabon yanayi, inda tun a cikin makon da ya gabata kotun ta karbe kujerar wakilin karamar Hukumar Tarauni, wanda a farko aka ayyana Jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ta lashe zaben. Sai dai sakamako bai yi wa Jam’iyyar APC dadi ba, dan takararta Honarabul Hafizu Ibrahim Kawu ya garzaya gaban kotu, inda ya kalubalanci rashin sahihancin sunan da dan takarar Jam’iyyar NNPP ke amfani da shi. Sakamakon wannan korafin, bayan sauraron bangarorin biyu, kotun ta yanke hukuncin mayarwa da Honarabul Hafizu Kawu wannan kujera.

  • Kotun Zaben Gwamnan Taraba: Cikin Matsi INEC Ta Ayyana Sakamako, A Sake Bitar Zaben – NNPP

Haka zalika, kotun ta sake karbe kujerar wakilin kananan Hukumomin Kura, Madobi da Garun Malam, wadda dan Jam’iyyar NNPP aka bayyana a matsayin wanda ya lashe zaben. Wanda ya yi wa Jam’iyyar APC takara, Honarabul Musa Iliyasu Kwankwaso ya garzaya kotu, inda ya zargi cewa dan takarar NNPP bai aje aikinsa ba kamar yadda dokokin hukumar zabe suka gindaya. Hakan ya sa kotun duba hujjojin da lauyoyin bangaren masu korafi suka gabatar, sannan kuma ta yanke hukuncin mayar wa Musa Iliyasu Kwnakwaso na Jam’iyyar APC a matsayin halastacen wanda ya lashe zaben.

Ita ma kujerar karamar Hukumar Kumbotso wadda tun farko aka ayyna Honarabul Idris Dan Kawu a matsayin wanda ya lashe zaben. Kotun sauraron korafe-korafen zaben ta kwace wannan nasara, inda ta tabbatar wa Honarabul Manniru Babba Dan Agundi a matsayin wanda ya lashe zaben tare da cin tarar Idris Dan Kawu naira 200,000.00 ko zaman gidan gyaran hali na watanni shida.

Zuwa yanzu jam’iyyar adawa ta APC ta samu nasarar karbe kujeru uku daga cikin kujerun da suke kalubalantar jam’iyyar NNPP kan ikirarin lashe zabensu, yanzu dai ko shakka babu kallo ya r koma sama, domin bisa ga dukkan alamu wankin hula na neman kai jam’iyya mai mulki ta NNPP dare, ta yadda ake masu dauki dai-dai a kujerun da suke ikirarin lashewa. Wanda kuma har yanzu akwai sauran wasu masu yawa da suke gaban kotu da jam’iyyar APC ke kalubalantar nasararsu.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Wanann hali da jam’iyyar NNPP ta tsinci kai a ciki ya sa wasu magoya bayanta fara sun tunanin me jagororin jam’iyyar NNPP ke ciki zuwa yanzu da suka zuba ido ana ta yi masu dauki dai-dai. Sannan wasu na ganin daman ‘yan takarkarun na Jam’iyyar ta NNPP ba a yi masu taza da tsifa ba kafin tsaryar da su takarar. Wannan ta sa a ganin wasu suke zargin daman ba mamaki an yi kitso da kwarkwata. Baya ga wannan ita Jam’iyyar NNPP daman a Jihar Kano kadai take da adadin kujerun da suke tinkaho da su kuma wasu na ganin takun sakar da jagoran darikar ta Kwankwasiyya, Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso ke yi da wasu shugabanni masu rike da madafun iko ya kara haifar wa da jam’iyyar tarnaki.

Yanzu dai masu fashin baki na ganin wannan karbe kujerun da jam’iyyar adawa ta APC ke yi na zaman wata ‘yar manuniya da ke haska hukuncin kotun da ake sauraron shari’ar da ake yi tsakanin Gwamna Abba Kabir Yusuf da kuma Dakta Nasiru Yusuf Gawuna na jam’iyyar APC, wanda a iya cewa ba a san maci tuwo ba sai miya ta kare.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: kanoKwankwasiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Babbar Darektar UNEP Ta Nuna Yabo Ga Matakan Kasar Sin Na Kiyaye Muhallin Halittu

Next Post

Sin Na Bin Diddigin Hasarar Rayuka Da Dukiyoyi Da Mahaukaciyar Guguwa Ta Haddasa A Gabashin Libya

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Da ɗumi-ɗuminsa

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

3 hours ago
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a
Labarai

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

5 hours ago
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
Labarai

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

6 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

8 hours ago
Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas
Labarai

Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas

12 hours ago
Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos
Labarai

Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos

13 hours ago
Next Post
Libya

Sin Na Bin Diddigin Hasarar Rayuka Da Dukiyoyi Da Mahaukaciyar Guguwa Ta Haddasa A Gabashin Libya

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.