Sakatare janar na kwamitin kolin jam’iyyar juyin juya hali ta al’ummar Laos wato LPRP, kuma shugaban kasar, Thongloun Sisoulith, ya gudanar da ziyara a kasar Sin tun daga ranar 2 zuwa 6 ga watan nan.
A yayin ziyararsa, shugabannin Sin da Laos sun amince da kara daukaka dangantakar dake tsakanin kasashen biyu zuwa sabon matsayi, da neman raya makomar bai daya tsakanin Sin da Laos a dukkan fannoni a sabon zamani.
Daukaka dangantakar dake tsakanin Sin da Laos, ba kawai zai taimaka ga bunkasa kasashen biyu, haka kuma zai amfana wa dukkanin duniya baki daya. A yayin ziyararsa a wannan karo, shugaba Thongloun ya bayyana cewa, kasar Sin ta riga ta kasance kasa mai jagorantar tsarin gurguzu da kasashe masu tasowa, da kuma ginshikin da ke kiyaye zaman lafiya da tsarin dogaro da bangarori da yawa a duniya.
Sin da Laos sun jaddada cewa, za su yi kokari tare wajen tabbatar da adalci a tsakanin kasa da kasa, sun kuma yi kira ga raya tsarin dogara da bangarori daban daban a duniya, da dunkulewar tattalin arzikin duniya baki daya yadda ya kamata, da kuma kara tabbatar adalci wajen gudanar da harkokin duniya. Hakan dai zai taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya da ci gaba a yankinsu har ma a duk duniya baki daya. (Zainab Zhang)















Discussion about this post