Jam’iyyar NDC ta sanar da cewa za ta fitar da sunayen masu neman takara da suka samu nasarar tsallake matakin tantancewa domin sayen fom ɗin tsayawa takara, a wani ɓangare na shirye-shiryenta na zaɓukan da ke tafe 2027.
Jam’iyyar ta ce fitar da jerin sunayen na daga cikin muhimman matakan da ake bi wajen zaɓen ƴan takara, inda waɗanda suka cika sharuɗɗa ne kawai za su samu damar ci gaba zuwa mataki na gaba na tsarin takara.
A cewar NDC, an tsara matakin ne domin tabbatar da gaskiya da kuma bin dokokin cikin gida da ƙa’idojin jam’iyyar wajen zaben ƴan takara.
Ta ƙara da cewa bayan fitar da jerin sunayen, za a sanar da ƙarin bayanai kan jadawalin sayen fom, da tantancewa da sauran matakan da za su kai ga zaƙulo ƴan takarar jam’iyyar a muƙamai daban-daban.














Discussion about this post