Wani jami’in rundunar tsaron al’umma ta Sokoto ya rasa ransa, yayin da aka yi garkuwa da mutane da dama bayan wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kai hari garin Sabon Birni da ke karamar hukumar Sabon Birni ta jihar Sokoto a daren Litinin.
Majiyoyi da dama sun tabbatar da faruwar lamarin, suna mai bayyana shi a matsayin sabon yunkurin da ‘yan bindiga ke yi na kutsawa cikin garin, wanda a halin yanzu ke karbar bakin gudun hijira da dama da suka rasa matsugunansu daga kauyukan da matsalar tsaro ta addaba.
Dan majalisar dokokin jihar Sokoto mai wakiltar mazaɓar Sabon Birni, Hon. Aminu Boza, ya tabbatar da harin, inda ya ce maharan sun yi garkuwa da mutane da dama.
Sai dai ya bayyana cewa har yanzu ba a tantance ainihin adadin mutanen da aka sace ba.















Discussion about this post