Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Kebbe/Tambuwal a Jihar Sakkwato, Honarabul Abdussamad Dasuki ya bayyana cewa hukumar zabe a karkashin jagorancin Joash Amupitan barazana ce ga dimokuradiyyar jam’iyyu da dama a Nijeriya.
Dan majalisar ya yi zargin cewa hukumar na yin hadin guiwa da wasu da ke kokarin danne jam’iyyun adawa domin mayar da Nijeriya kasa mai jam’iyya daya kacal.
- Xi Ya Bukaci Zurfafa Akidun Siyasa A Rundunonin Sojin Kasar
- Rikicin Bashin ₦25,000 Ya Yi Sanadin Kashe Wani Matashi A Mashaya Giya
Ya bayyana hakan ne a ranar Laraba lokacin da ya karbi katin zama dan jam’iyyar ADC a mazabarsa ta Dogon Daji/Salah da ke karamar hukumar Tambuwal a jihar Sakkwato.
Da yake jawabi ga taron magoya bayansa, dan majalisar ya yi gargadin cewa sabbin abubuwan da ke faruwa a fagen siyasar Nijeriya na nuni da wani tsari da aka tsara domin raunana muryoyin ‘yan adawa da kuma tauye ginshikin dimokuradiyya.
Ya yi nuni musamman da matakin da hukumar zabe ta dauka na kin amincewa da shugabancin jam’iyyar ADC a karkashin David Mark, yana mai cewa wannan wani muhimmin mataki ne a abin da ya kira wani shiri na danne ‘yan adawa da rushe tsarin dimokuraɗiyyar jam’iyyu da dama.
A cewarsa wannan mataki an yi shi ne domin raunana tsarin jam’iyyun adawa, lalata tsarin jam’iyyu da yawa, tare da kai kasar zuwa ga tsarin jam’iyya daya kacal, inda jam’iyyar APC za ta zama ba kawai mafi karfi ba, har ma ita kadai ce za ta iya tsayar da dan takara mai karfi a zaben shugaban kasa a 2027.
Ya ce wannan ba batun jam’iyya daya ko rikicin shugabanci kadai ba ne, ya ce batu ne da ya shafi makomar dimokuraɗiyya.
Ya ce abin da ake gani a yanzu wani tsari ne da aka tsara domin rufe bakin ‘yan adawa, takaita sararin dimokuraɗiyya da kuma tilasta tsarin jam’iyya daya a kasa mai yawaitar bambance – bambance.
Ya kuma yi gargadin cewa irin wadannan matakai, idan ba a dakatar da su ba, na iya mayar da kasar baya a nasarorin mulkin dimokuradiyya da Nijeriya ta samu a tsawon shekaru.
Dan majalisar ya yi kira ga al’umma, kungiyoyin fararen hula da kuma kasashen duniya da su kasance cikin shiri, ya ce duk masu ruwa da tsaki da su tashi tsaye wajen kare cibiyoyin dimokuraɗiyya tare da tabbatar da bin doka da oda a Nijeriya.















Discussion about this post