‘Yansanda a Jihar Jigawa sun kama wasu mutane da ake zargi da aikata laifukan satar mutane, fashi da makami, sata, da kuma satar dabbobi a jihar.
Kakakin ‘yansandan jihar, Shi’isu Adam, ya ce an kama waɗanda ake zargin ne a wurare daban-daban bayan samun bayanan sirri.
Daga cikin waɗanda aka kama akwai mutum uku da ake zargi da fashi da makami a yankin masarautar Hadeja.
‘Yansanda sun ce sun gano bindiga ƙirar AK-47 da aka ƙera a gidan ɗaya daga cikin waɗanda ake zargin, kuma ana ci gaba da bincike domin kama sauran abokan aikinsu.
A wani aiki na daban, an kama wasu mutum biyu da ake zargi da shirin satar mutane kafin su aiwatar da laifin.
Bincike ya nuna cewa sun taɓa aikata irin wannan laifi a baya.
A ƙaramar hukumar Gwaram, an kama wasu mutum biyu da suka sace tumaki, yayin da a Taura kuma aka kama wasu mutum biyu kan satar dabbobi, inda aka gano wasu tumaki a hannunsu.
‘Yansanda kuma sun daƙile wani harin fashi da makami a hanyar Ringim zuwa Chaichai, inda aka kama mutum ɗaya a wajen, sannan aka kama wasu daga baya.
Haka kuma, an gano wasu babura da aka sace a Dutse da wasu wurare bayan waɗanda ake zargin sun tsere.
Kwamishinan ‘yansandan jihar, Haruna Yahaya, ya yaba wa jami’an da suka gudanar da aikin, yana mai cewa rundunar na ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da tsaro a jihar.
Ya kuma buƙaci al’umma da su riƙa ba da bayanai da wuri domin taimakawa wajen hana aikata laifuka.














Discussion about this post