Za a gudanar da taron tattaunawa kan zuba jari da kasuwanci na sassan kasa da kasa na kasar Sin wato CIFIT karo na 26 daga ranar 8 zuwa 11 ga watan nan a birnin Xiamen na lardin Fujian da ke kudancin kasar Sin, inda sassan gwamnati gami da tawagogin kamfanonin masana’antu da cinikayya sama da 1200 daga kasashe da yankuna 129 gami da kungiyoyin kasa da kasa 30 suka yi rajistar halarta.
A wajen taron manema labarai da aka yi da yammacin jiya 6 ga watan nan, mataimakin shugaban sashin kula da harkokin bunkasa zuba jari na ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin, Yu Guangsheng, ya bayyana cewa, taken dindindin na taron shi ne, “fadada zuba wa juna jari, da samar da ci gaba ga duniya baki daya”, wanda ke kunshe da wasu muhimman fannoni uku da suka hada da “zuba jari a kasar Sin”, da “zuba jari da Sin take yi a kasashen waje” gami da “zuba jari tsakanin kasa da kasa”, inda aka kebe wasu yankunan nune-nune na musamman guda 14 masu fadin murabba’in mita dubu 200, da shirya wasu ayyuka na musamman guda 46 gami da bukukuwan tallata ayyukan taron guda 52.
Jami’in ya kara da cewa, taron na bana zai kara mayar da hankali kan harkokin zuba wa juna jari, da sa kaimi ga jawo jarin waje gami da zuba jari a kasashen waje, don su samu ci gaba tare kuma ta hanyar da ta dace. (Murtala Zhang)














