Lauya mai rajin kare haƙƙin ɗan adam, Femi Falana, ya ce dole Nijeriya ta magance matsalolin tattalin arziƙi da tsaro idan tana son kaucewa juyin mulki.
Da yake magana a gidan talabijin na Channels, Falana ya ce talauci, jahilci da rashin tsaro su ne manyan dalilan da ke haifar da rashin kwanciyar hankali.
- Ma’aikatar Wajen Sin: Shin Japan Tana Yunkurin Ci Zarafin Sin Tare Da Haifar Da Tashin Hankali
- IGP Ya Yi Kira Da A Ƙara Ƙaimi Wajen Yaƙi Da Labaran Ƙarya
Ya yi gargaɗin cewa dimokuraɗiyya ba za ta bunƙasa ba idan ana hukunta mutane saboda bayyana ra’ayinsu.
Falana ya yi kira ga INEC da ta bai wa jam’iyyu masu aƙida daban-daban damar shiga fagen siyasa.
Ya ce shugabanni da dama a Afirka suna rauni ta fannin adawa, wanda kan jawo tashin hankali da juyin mulki.
Ya ƙara da cewa juyin mulki zai ci gaba da faruwa idan gwamnati tana ɗaure, korar ko cutar da shugabannin adawa.
Falana ya buƙaci Nijeriya ta nuna jagoranci a yankin ta hanyar inganta dimokuraɗiyya ta gaskiya.
Maganarsa ta biyo bayan yunƙurin juyin mulki da aka yi a Jamhuriyar Benin, inda dakarun ECOWAS suka taimaka wajen daƙile yunƙurin.













