Wata Babbar Kotun Tarayya dake ƙasar Canada ta jaddada matakin hana ɗan wasan tsakiyar Ghana, Thomas Partey, shiga ƙasar gabanin wasan buɗe gasar cin kofin duniya na shekarar 2026 da Ghana ta fafata da Panama ranar Laraba.
An yanke wannan hukuncin ne ranar Talata biyo bayan sauraron ƙarar da lauyoyin Partey suka ɗaukaka, inda suka nemi a soke matakin hana shi biza wanda ya hana tsohon ɗan wasan tsakiyar na Arsenal tafiya birnin Toronto tare da sauran ƴan wasan Ghana. Matsalar bizar ɗan wasan mai shekaru 33 ta samo asali ne sakamakon shari’ar laifuka da ake gudanarwa a Birtaniya, wadda ta haɗa da tuhumar fyaɗe guda bakwai da kuma zargin cin zarafi a guda ɗaya, dangane da zargin da mata huɗu suka yi masa tsakanin shekarar 2020 da 2022, lokacin da yake wasa a ƙungiyar Arsenal.
Partey, wanda a yanzu haka yake buga wa Ɓillareal wasa ya ce ba shi da laifi a dukkan tuhume-tuhumen, kuma an tsara gudanar da shari’ar a ƙarshen wannan shekarar. To sai dai kuma, matakin da kotun ta ɗauka na nufin Partey ba zai iya shiga ƙasar Canada ba, lamarin da ya zama babban rashi ga tawagar ƙwallon ƙafar Ghana gabanin wasansu da Panama.















Discussion about this post