Wasu da ake zargi ’yan ta’adda ne sun kai farmaki da tsakar dare a garin Tsamiya da ke Ƙaramar Hukumar Bagudo a jihar Kebbi, inda suka sace mazaunin yankin guda daya tare da ƙona sansanin jami’an tsaro na NSCDC. Kakakin rundunar ‘yansandan jihar Kebbi, SP Bashir Usman, ne ya tabbatar da aukuwar lamarin cikin wata sanarwa da ya fitar, inda ya bayyana cewa hararin ya jefa mazauna garin cikin fargaba da firgici.
Kakakin ya bayyana sunan mutumin da aka yi garkuwa da shi a matsayin Alhaji Yusuf Bazamfare, wanda maharan suka tafi da shi bayan sun mamaye garin suna harbe-harbe ba kaukautawa. Haka kuma, ’yan ta’addan sun banka wa wani shingen bincike na wucin gadi na jami’an NSCDC wuta, gami da gidan wani mazaunin garin mai suna Sule Mai Goge.
Bayan faruwar lamarin, Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kebbi ya ba da umarnin tura ƙarin jami’an tsaro cikin gaggawa zuwa yankin da abin ya shafa domin ƙarfafa tsaro da kuma kare rayuka da dukiyoyin al’umma. A halin yanzu, rundunar ‘yansanda tare da haɗin gwuiwar sauran hukumomin tsaro sun ƙaddamar da gagarumin bincike da sumame na haɗin gwuiwa da nufin ceto mutumin da aka sace.
Daga ƙarshe, rundunar ta yi kira ga ɗaukacin mazauna yankin da su kwantar da hankulansu, kuma su ci gaba da ba wa jami’an tsaro sahihan bayanai na sirri domin taimaka musu wajen daƙile ayyukan laifuka da dawo da zaman lafiya a jihar. Haka kuma, an tabbatar da cewa za a yi dukkan mai yiwuwa domin kamo waɗanda ke da hannu a hararin don fuskantar hukunci.














Discussion about this post