Jigo a jam’iyyar ADC a jihar Kano kuma mai neman takarar gwamna, Alhaji Ibrahim Ali Amin Little, ya nesanta kansa da zargin cewa ana ƙaƙaba wa jam’iyyar shugabanni ko ‘yan takara ba bisa ƙa’ida ba. Ibrahim Little ya bayyana cewa dukkan matakan da ake ɗauka a halin yanzu suna tafiya ne da ƙa’idojin kundin tsarin mulkin jam’iyyar, saɓanin jita-jita da wasu ke yaɗawa.
Tsohon ɗan takarar ya zargi wasu mambobin jam’iyyar da gangancin ƙirƙirar labaran ƙarya da nufin haddasa ruɗani da kuma raba kan ƴan jam’iyyar. A cewarsa, waɗannan mutane suna amfani da kafafen yaɗa labarai domin ɓatanci ga taron sasancin da aka gudanar, da nufin haɗa kan mambobin jam’iyyar gabanin zaɓuka masu zuwa.
Ibrahim Little ya jaddada cewa babu wani mutum guda da ke da ikon juya akalar jam’iyyar ko sanya mata dokoki na ƙashin kansa, domin komai yana tafiya ne ƙarƙashin amincewar shugabannin ADC na ƙasa . Ya kuma yi kira ga mambobin jam’iyyar da su guji biye wa kalaman ɓatanci, maimakon haka su mayar da hankali wajen gina tsarin da zai tabbatar da adalci da cigaban jam’iyyar a jihar Kano.
Daga ƙarshe, ya bayyana cewa ƙofarsa a buɗe take ga tattaunawa ta gaskiya da dukkan ɓangarorin da ke da ƙorafi, muddin hakan zai kawo zaman lafiya. Ya tabbatar wa da magoya bayansa cewa ADC za ta fito da ƙarfinta kuma za ta tsayar da sahihan ‘yan takara ta hanyar dimokuraɗiyya ta gaskiya ba tare da danne haƙƙin kowa ba.















Discussion about this post