ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

by Abubakar Sulaiman
59 minutes ago

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

Jigo a jam’iyyar ADC a jihar Kano kuma mai neman takarar gwamna, Alhaji Ibrahim Ali Amin Little, ya nesanta kansa da zargin cewa ana ƙaƙaba wa jam’iyyar shugabanni ko ‘yan takara ba bisa ƙa’ida ba. Ibrahim Little ya bayyana cewa dukkan matakan da ake ɗauka a halin yanzu suna tafiya ne da ƙa’idojin kundin tsarin mulkin jam’iyyar, saɓanin jita-jita da wasu ke yaɗawa.

Tsohon ɗan takarar ya zargi wasu mambobin jam’iyyar da gangancin ƙirƙirar labaran ƙarya da nufin haddasa ruɗani da kuma raba kan ƴan jam’iyyar. A cewarsa, waɗannan mutane suna amfani da kafafen yaɗa labarai domin ɓatanci ga taron sasancin da aka gudanar, da nufin haɗa kan mambobin jam’iyyar gabanin zaɓuka masu zuwa.

Ibrahim Little ya jaddada cewa babu wani mutum guda da ke da ikon juya akalar jam’iyyar ko sanya mata dokoki na ƙashin kansa, domin komai yana tafiya ne ƙarƙashin amincewar shugabannin ADC na ƙasa . Ya kuma yi kira ga mambobin jam’iyyar da su guji biye wa kalaman ɓatanci, maimakon haka su mayar da hankali wajen gina tsarin da zai tabbatar da adalci da cigaban jam’iyyar a jihar Kano.

ADVERTISEMENT

Daga ƙarshe, ya bayyana cewa ƙofarsa a buɗe take ga tattaunawa ta gaskiya da dukkan ɓangarorin da ke da ƙorafi, muddin hakan zai kawo zaman lafiya. Ya tabbatar wa da magoya bayansa cewa ADC za ta fito da ƙarfinta kuma za ta tsayar da sahihan ‘yan takara ta hanyar dimokuraɗiyya ta gaskiya ba tare da danne haƙƙin kowa ba.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina
  • Abubakar Sulaiman
    Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga
  • Abubakar Sulaiman
    Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

June 21, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna
Manyan Labarai

Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna

June 21, 2026
Next Post
Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

June 21, 2026
Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

June 21, 2026
Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

June 21, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

June 21, 2026
Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu

Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu

June 21, 2026
Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.