Tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana dalilin da ya sa shugabannin siyasar Arewa suka amince da Peter Obi a matsayin wanda za su mara wa baya a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Da yake magana a gidan talabijin na Arise News a daren ranar Litinin, Kwankwaso ya ce shugabannin Arewa sun tattauna domin nemo ɗan takarar da yake da ƙwarewa, kuma daga ƙarshe suka ga Peter Obi ne ya fi dacewa.
Ya ce, “Na gana da shugabanninmu a Arewa domin neman wanda ya cancanta, kuma muka fahimci cewa Peter Obi ne ya fi dacewa. Shi ya sa muka amince mu yi aiki tare.”
Kwankwaso ya ce tun kafin su sanar da jama’a, tuni tafiyar Kwankwasiyya da magoya bayan Obi, wato Obidients, suka fara aiki tare.
Ya ce sun kafa wata haɗaka da suke kira “OK”.A cewarsa, sunan ya samo asali ne daga yadda wasu magoya baya ke cewa “OK” yayin da wasu ke cewa “KO”, kafin daga baya suka haɗa kai.
Ya kuma bayyana cewa tattaunawar haɗakar ta fara ne a cikin jam’iyyar ADC kafin daga baya su koma NDC domin ƙaƙƙarfan haɗakar adawa kafin zaɓen 2027.
Kwankwaso ya ƙaryata zargin cewa akwai saɓani tsakanin magoya bayan ɓangarorin biyu, yana mai cewa dukkanin ɓangarorin suna da biyayya kuma suna aiki tare, har da magoya bayansu da ke ƙasashen waje.














Discussion about this post