Rundunar ‘Yansandan Nijeriya ta sanar da kama wasu da ake zargi ‘yan fashi ne da kuma masu satar babura, tare da kwato makamai, alburusai, baburan sata da shanu da aka sace a wasu jerin ayyukan samane da aka gudanar a Jihar Kebbi.
Da yake ganawa da manema labarai ranar Litinin a hedikwatar ‘yansanda ta jihar, Kwamishinan ‘Yansanda, Umar M. Hadejia, ya ce an samu nasarorin ne ta hanyar sintiri bisa bayanan sirri, ƙarfafa hadin gwiwa da al’umma da kuma haɗin gwiwar jami’an tsaro daban-daban.
“Tun bayan da na karɓi aiki a matsayin Kwamishinan ‘Yansanda a ranar 12 ga Janairu, 2026, na zagaya sassan jihar tare da kafa sashen mayar da martanin gaggawa kan masu aikata muggan laifuffuka domin sabunta ƙudirin tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa a Jihar Kebbi,” in ji shi.
Hadejia ya ƙara da cewa jihar na fuskantar manyan barazanar tsaro, ciki har da fashi da makami, satar shanu, satar babura da kuma ayyukan wasu ƙungiyoyi kamar Lakurawa a yankunan kan iyaka.















Discussion about this post