Kasar Sin ta daga wani gini a otel na Mena House na kasar Masar, domin tunawa da rattaba hannu kan Sanarwar Cairo.Ofishin jakadancin Sin a Masar ne ya sanar da hakan jiya Lahadi, inda ya ce yanzu haka ana gyara wurin ginin, kuma za a bude shi ga jama’a bayan aikin ya kammala.
Sanarwar ta Cairo na zaman muhimmiya a tarihi mai kuma karfin doka, wadda ke tabbatar da matsayin Taiwan na wani yanki na kasar Sin da ba zai iya ballewa ba.
A shekarar 1943 ne kasashen Sin da Amurka da Birtaniya suka fitar da Sanarwar Cairo a otel na Mena House na Masar, inda suka ayyana cewa, a kwace dukkan tsibiran da ke yankin Pasifik daga hannun Japan, watau tsibiran da ta kwace ko ta mamaye tun daga barkewar yakin duniya na I a shekarar 1914, haka kuma a mayar da dukkan yankunan da Japan ta kwace daga wajen Sinawa kamar Manchuria da Formosa da Pescadores.
A ranar 26 ga watan Yulin shekarar 1945 kuma, kasashen Sin da Amurka da Birtaniya suka rattaba hannu kan Sanarwar Potsdam, wadda Tarayyar Soviet ita ma ta amince da ita. Sanarwar ta yi kira da a aiwatar da tanade-tanaden Sanarwar Cairo.
A watan Satumban wannan shekara kuma, Japan ta rattaba hannu kan yarjejeniyar mika wuya, inda ta yi alkawarin za ta cika dukkan ka’idojin da Sanarwar Potsdam ta zayyana. Dukkan wadannan jerin daftarori masu karfin doka, sun tabbatar da ikon Sin kan yankin Taiwan, wanda wani muhimmin bangare ne na odar duniya bayan yakin duniya na II. (Fa’iza Mustpha)















Discussion about this post