Jiga-jigan jam’iyyar adawa ta ADC sun fito kan tituna a safiyar Laraba suna gudanar da zanga-zanga kan abin da suka kira nuna bangaranci daga hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa (INEC).
Zanga-zangar, wadda ke gudana a Abuja, ta haɗa da jerin gwanon masu zanga-zangar zuwa shalkwatar INEC da ke babban birnin tarayya.
Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana zanga-zangar a matsayin ta lumana, yana mai cewa manufarta ita ce kare dimokuraɗiyya da kuma hana kafa mulkin kama-karya.
- INEC Ta Gyara Jadawalin Zaben 2027 Tare Da Tsawaita Wa’adin Mika Rajistar Jam’iyyun Siyasa
- INEC Ta Gyara Jadawalin Zaben 2027 Tare Da Tsawaita Wa’adin Mika Rajistar Jam’iyyun Siyasa
A cikin jerin gwanon akwai tsohon gwamnan Jihar Anambra, da Peter Obi; da tsohon shugaban majalisar dattawa, da Sanata David Mark; da jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso; da sauran manyan ’yan siyasa da dama.
Haka kuma, masu fafutukar gyaran tsarin zaɓe da dubban magoya bayan jam’iyyar ADC sun halarci zanga-zangar, yayin da ake sa ran ƙarin bayani kan lamarin nan gaba kaɗan.















Discussion about this post