Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Radda, na jagorantar wani taron gaggawa na Majalisar Tsaro a gidan Gwamnati da ke Katsina.
Taron na ranar Litinin ya haɗa shugabannin hukumomin tsaro a jihar, shugabannin ƙananan hukumomin da abin ya shafa, da wakilai daga Rundunar Sojin Nijeriya, Hedikwatar Tsaro, da Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS).
Haka kuma, akwai jami’ai daga Rundunar ’Yansandan Nijeriya (NPF), Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya (NIS), Hukumar Tsaro da Kariya ta Farin Kaya (NSCDC), Hukumar Kwastam ta Nijeriya (NCS), Hukumar Kula da Hanyoyi ta Tarayya (FRSC), Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya (FFS), da Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA), da KSCWC.
Kwamishinan Tsaron Cikin Gida da Harkokin Gida, tare da fitattun sarakunan gargajiya, shugabannin addini, da manyan jami’an gwamnati ma sun halarci taron.













Discussion about this post