Iran ta ƙi amincewa da wata shawarar tsagaita wuta a yaƙinta da Amurka da Isra’ila, kamar yadda kafafen yaɗa labarai na kasar Iran suka ruwaito a ranar Litinin, duk da barazanar da Shugaban Amurka Donald Trump ya yi na lalata muhimman ababen more rayuwarta.
“Iran ta isar wa Pakistan da martaninta kan shawarar Amurka na kawo ƙarshen yaƙin,” in ji kamfanin dillancin labarai na IRNA, ba tare da bayyana abin da tayin Amurka ya ƙunsa ba.
“A cikin wannan martani—wanda aka gabatar cikin shawarwari goma—Iran ta yi watsi da su, inda ta nace cewa, tana kan bukatar kawo ƙarshen rikicin gaba ɗaya.”
Kasashe da dama na ƙoƙarin samo mafita ta diflomasiyya domin kawo ƙarshen yaƙin kwanaki 38 da hare-haren Isra’ila da Amurka suka tayar, yayin da Iran ke mayar da martani ta hanyar harba makamai masu linzami zuwa wurare daban-daban a Gabas ta Tsakiya.















Discussion about this post