ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunƙurin Juyin Mulki: Hafsoshin Soji 16 Za Su Fuskanci Hukunci

by Sulaiman
5 months ago
Juyin mulki

Hafsoshin Sojin Nijeriya aƙalla 16 ne za su fuskanci hukuncin kisa ko ɗaurin rai-da-rai bisa laifin yunƙurin hamɓarar da gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

 

Rundunar Sojin Nijeriya ta sanar da cewa binciken da ta kammala bayan tsare waɗanda ake zargin ya same su da laifin yunƙurin kifar da gwamnati.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 11 Yayin Da Ake Kallon Ƙwallo A Mexico
  • Da Gaske Ne Babu Tashar Samar Da Lantarki Ta Karfin Iska A Kasar Sin?

Wasu tsofaffin Hafsoshin sojin Nijeriya sun bayyana cewa hukuncin kisa shi ne abin da dokar aikin sojin ƙasar ta tanada kan duk wanda aka samu da hannu a yunƙurin juyin mulki.

 

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

A watan Oktoban bara ne rahoto ya ɓulla cewa, Rundunar Sojin Nijeriya, ta hannun Hukumar Binciken Leƙen Asiri ta Soji (DIA) ta tsare wasu hafsoshinta 16 masu muƙamin Kyaftin zuwa Birgediya-Janar kan zargin yunƙurin yi wa Shugaba Tinubu juyin mulki.

 

An ruwaito a ranar Litinin cewa kwamitin da rundunar ta kafa ya kammala bincikensa tare da miƙa rahotonsa ga Shugaba Tinubu domin ɗaukar mataki na gaba.

 

Daraktan Yaɗa Labarai na Hedikwatar Tsaro ta Nijeriya, Manjo-Janar Samaila Uba, ya tabbatar cewa kwamitin ya miƙa rahotonsa ga “mahukuntan da suka dace.”

 

Sanarwar da Manjo-Janar Samaila Uba ya fitar a ranar Litinin ta ce za a gurfanar da waɗanda aka samu da laifi a gaban kotun soji domin yanke musu hukuncin da dokokin aikin soji suka tanadar.

 

Ya bayyana cewa an sanar da jama’a halin da ake ciki ne domin komai ya kasance a fili da kuma tabbatar da adalci, a yayin da rundunar za ta kiyaye ƙa’idojin aikinta cikin ƙwarewa, da kuma biyayya da kare dokar ƙasa.

 

Ya ce doka ce ta tanadar da matakan ladabtarwa da aka ɗauka domin tabbatar da ɗa’a da kuma ƙwarewa a tsakanin jami’an rundunar.

Juyin mulki
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Ana Maraba Da ‘Yan Jarida Na Cikin Gida Da Na Ketare Ga Taron NPC da CPPCC Da Sin Za Ta Gudanar

Ana Maraba Da 'Yan Jarida Na Cikin Gida Da Na Ketare Ga Taron NPC da CPPCC Da Sin Za Ta Gudanar

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.