‘Yan bindiga sun buɗe wuta kan jama’a da ke tsaka da kallon wasan ƙwallo a wani yanki na tsakiyar ƙasar Mexico, inda suka kashe mutane 11 tare da jikkata wasu 12.
Magajin garin Salamanca, Cesar Prieto, ya ce harin ya faru ne kusa a daidai lokacin ƙarshen wasan, lokacin da ‘yan bindigar suka shiga filin suka fara harbi.
- Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Fashi da Makami A Abuja, Sun Kama Wani Mutum
- Ƙwace Mulki A Hannun Tinubu Ne Kaɗai Hanyar Ceto Nijeriya A 2027 — ADC
Wasu daga cikin waɗanda suka jikkata na karɓar kulawa a asibiti, yayin da har yanzu babu wata ƙungiya da ta ɗauki alhakin kai harin.
Mahukunta sun ce suna zargin miyagun ƙungiyoyi masu safarar ƙwayoyi ne ke da hannu a wannan hari, kasancewar ta’addanci na ƙaruwa a wasu sassan ƙasar.
Mexico na cikin ƙasashe uku da za su karɓi baƙuncin wasu daga cikin wasannin gasar cin kofin duniya, lamarin da ke sa mutane nuna damuwa kan tsaro.















Discussion about this post