Jam’iyyar ADC ta buƙaci Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta (INEC) da ta ƙara mata lokaci domin gudanar da zaɓukan fidda gwani, yayin da ta bayyana shirinta na fitar da jadawalin zaɓukan cikin wannan mako.
Sakataren tsare-tsare na ƙasa na jam’iyyar, Chinedu Idigo, ne ya bayyana hakan ranar Juma’a yayin wata hira da LEADERSHIP a Abuja.
Ya jaddada cewa duk da ana ci gaba da shirye-shirye, ana buƙatar ƙarin lokaci domin tabbatar da an gudanar da ingatattun zaɓukan fidda gwani ga dukkan muƙaman zaɓe.
Idigo ya bayyana cewa rikicin cikin gida da kuma doguwar shari’ar da jam’iyyar ta fuskanta sun matuƙar kawo cikas ga jadawalinta, lamarin da ya rage mata lokaci wajen kammala muhimman shirye-shiryen kafin zaɓe.
Ya kafa hanzari da cewa adalci da kare martabar dimokuraɗiyya na buƙatar INEC ta ƙara wa jam’iyyar wa’adin domin ta samu damar gudanar da ayyukanta yadda ya kamata.















Discussion about this post