ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 29, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zama Lafiya Ya Fi Zama Dan Sarki!

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 months ago

Tun kafin barkewar tashin hankali na baya bayan nan a gabas ta tsakiya, masharhanta suke ta bayyana damuwa game da yiwuwar fuskantar mummunan yanayi idan har ba a kai zuciya nesa ba.

Masana da dama sun yi hasashen bazuwar tasirin yakin a dukkanin sassan gabas ta tsakiya, muddin Amurka ta kaddamar da hare-hare kan Iran.

To sai dai ana tsaka da tattaunawa, sai kwatsam Amurka da Isra’ila suka fara kaddamar da hare-hare kan kasar ta Iran, nan take kuma Iran din ta fara mayar da martani kan kawayen Amurka dake samar mata da sansanonin kaiwa Iran din hare-hare dake yankin baki daya.

ADVERTISEMENT

Wannan lamari ya kasance mafari na dauki ba dadi da aka kwashe sama da kwanaki 40 ana yi, kafin cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta makwanni biyu, aka kuma fara tattaunawar da ba ta kai ga haifar da sakamakon da ake fata ba.

Tattaunawar da aka gudanar tsakanin wakilan Amurka da na Iran a ranar 14 ga watan nan a kasar Pakistan, ta zamo irinta ta farko tun bayan barkewar rikicin, kuma a yanzu haka, gabanin sake tattaunawa a karo na biyu, Amurka ta yi ikirarin toshe tashohin jiragen ruwa dake Iran a dukkan fannoni, a wani mataki da sassan kasa da kasa ke ganin zai kara tsananta halin da ake ciki.

LABARAI MASU NASABA

Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

Yayin da ake fatan ganin sassan biyu sun sake gudanar da tattaunawa ta kai tsaye kuma cikin nasara, wani abun lura shi ne yadda wannan danbarwa ta haifar da mummunan tasiri ga tattalin arzikin duniya baki daya, ba wai kawai kasashen dake shiyyar ta gabas ta tsakiya ba.

Mun dai ga yadda wannan tashin hankali ya gurgunta tsarin gudanar hada-hadar cinikayya na duniya, ciki har da na kasashen yammacin duniya masu karfin ci gaba.

Rufe mashigin Hormuz, ya illata hada-hadar albarkatun makamashi na duniya, wanda hakan ya haifar da hauhawar farashin albarkatun mai a kasuwannin duniya, da tsadar kayayyaki a kusan dukkanin kasashe, ciki har da masu tasowa wadanda da dama can ke cikin yanayi na matsi.

Hakan kuma na da nasaba da yadda makamashi ke da alakar kai tsaye da harkokin sufuri, da sarrafa hajojin masana’antu, da rarraba hajojin zuwa sassan kasa da kasa, da noma, da sayayyar ababen bukatun al’umma na yau da kullum.

Wani muhimmin darasi game da wannan tashin hankali, da ya kai ga rufe mashigin Hormuz, shi ne rashin kwanciyar hankali a wani bangare na duniya, na iya haifar da mummunan tasiri ga duniya baki daya.

Wato dai wannan yaki na gabas ta tsakiya ya zamewa duniya darasi game da muhimmancin tabbatar da zaman lafiya, da walwala a dukkanin sassan kasa da kasa.

Kamar dai yadda Bahaushe kan ce “Zama Lafiya Ya Fi Zama Dan Sarki!”Wannan danbarwa ta zamewa duniya babban kalubale, ta yadda tasirin tashin hankalin na gabas ta tsakiya bai takaita ga yankin kadai ba, maimakon hakan ya haifar da matsalar tattalin arziki da mai yiwuwa a jima ana dandana illar ta. (Saminu Alhassan)

Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao
  • Sulaiman
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu
  • Sulaiman
    Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya

MASU ALAKA

Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao
Daga Birnin Sin

Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

June 28, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu
Daga Birnin Sin

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

June 28, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026
Next Post
Tanzania Na Shirin Jan Hankalin Adadi Mai Yawa Na Sinawa Masu Yawon Bude Ido

Tanzania Na Shirin Jan Hankalin Adadi Mai Yawa Na Sinawa Masu Yawon Bude Ido

LABARAI MASU NASABA

Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

June 28, 2026
Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

June 28, 2026
An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

June 28, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

June 28, 2026
Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

June 28, 2026
Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

June 28, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.