Tun kafin barkewar tashin hankali na baya bayan nan a gabas ta tsakiya, masharhanta suke ta bayyana damuwa game da yiwuwar fuskantar mummunan yanayi idan har ba a kai zuciya nesa ba.
Masana da dama sun yi hasashen bazuwar tasirin yakin a dukkanin sassan gabas ta tsakiya, muddin Amurka ta kaddamar da hare-hare kan Iran.
To sai dai ana tsaka da tattaunawa, sai kwatsam Amurka da Isra’ila suka fara kaddamar da hare-hare kan kasar ta Iran, nan take kuma Iran din ta fara mayar da martani kan kawayen Amurka dake samar mata da sansanonin kaiwa Iran din hare-hare dake yankin baki daya.
Wannan lamari ya kasance mafari na dauki ba dadi da aka kwashe sama da kwanaki 40 ana yi, kafin cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta makwanni biyu, aka kuma fara tattaunawar da ba ta kai ga haifar da sakamakon da ake fata ba.
Tattaunawar da aka gudanar tsakanin wakilan Amurka da na Iran a ranar 14 ga watan nan a kasar Pakistan, ta zamo irinta ta farko tun bayan barkewar rikicin, kuma a yanzu haka, gabanin sake tattaunawa a karo na biyu, Amurka ta yi ikirarin toshe tashohin jiragen ruwa dake Iran a dukkan fannoni, a wani mataki da sassan kasa da kasa ke ganin zai kara tsananta halin da ake ciki.
Yayin da ake fatan ganin sassan biyu sun sake gudanar da tattaunawa ta kai tsaye kuma cikin nasara, wani abun lura shi ne yadda wannan danbarwa ta haifar da mummunan tasiri ga tattalin arzikin duniya baki daya, ba wai kawai kasashen dake shiyyar ta gabas ta tsakiya ba.
Mun dai ga yadda wannan tashin hankali ya gurgunta tsarin gudanar hada-hadar cinikayya na duniya, ciki har da na kasashen yammacin duniya masu karfin ci gaba.
Rufe mashigin Hormuz, ya illata hada-hadar albarkatun makamashi na duniya, wanda hakan ya haifar da hauhawar farashin albarkatun mai a kasuwannin duniya, da tsadar kayayyaki a kusan dukkanin kasashe, ciki har da masu tasowa wadanda da dama can ke cikin yanayi na matsi.
Hakan kuma na da nasaba da yadda makamashi ke da alakar kai tsaye da harkokin sufuri, da sarrafa hajojin masana’antu, da rarraba hajojin zuwa sassan kasa da kasa, da noma, da sayayyar ababen bukatun al’umma na yau da kullum.
Wani muhimmin darasi game da wannan tashin hankali, da ya kai ga rufe mashigin Hormuz, shi ne rashin kwanciyar hankali a wani bangare na duniya, na iya haifar da mummunan tasiri ga duniya baki daya.
Wato dai wannan yaki na gabas ta tsakiya ya zamewa duniya darasi game da muhimmancin tabbatar da zaman lafiya, da walwala a dukkanin sassan kasa da kasa.
Kamar dai yadda Bahaushe kan ce “Zama Lafiya Ya Fi Zama Dan Sarki!”Wannan danbarwa ta zamewa duniya babban kalubale, ta yadda tasirin tashin hankalin na gabas ta tsakiya bai takaita ga yankin kadai ba, maimakon hakan ya haifar da matsalar tattalin arziki da mai yiwuwa a jima ana dandana illar ta. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post