ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zama Lafiya Ya Fi Zama Dan Sarki!

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 months ago

Tun kafin barkewar tashin hankali na baya bayan nan a gabas ta tsakiya, masharhanta suke ta bayyana damuwa game da yiwuwar fuskantar mummunan yanayi idan har ba a kai zuciya nesa ba.

Masana da dama sun yi hasashen bazuwar tasirin yakin a dukkanin sassan gabas ta tsakiya, muddin Amurka ta kaddamar da hare-hare kan Iran.

To sai dai ana tsaka da tattaunawa, sai kwatsam Amurka da Isra’ila suka fara kaddamar da hare-hare kan kasar ta Iran, nan take kuma Iran din ta fara mayar da martani kan kawayen Amurka dake samar mata da sansanonin kaiwa Iran din hare-hare dake yankin baki daya.

ADVERTISEMENT

Wannan lamari ya kasance mafari na dauki ba dadi da aka kwashe sama da kwanaki 40 ana yi, kafin cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta makwanni biyu, aka kuma fara tattaunawar da ba ta kai ga haifar da sakamakon da ake fata ba.

Tattaunawar da aka gudanar tsakanin wakilan Amurka da na Iran a ranar 14 ga watan nan a kasar Pakistan, ta zamo irinta ta farko tun bayan barkewar rikicin, kuma a yanzu haka, gabanin sake tattaunawa a karo na biyu, Amurka ta yi ikirarin toshe tashohin jiragen ruwa dake Iran a dukkan fannoni, a wani mataki da sassan kasa da kasa ke ganin zai kara tsananta halin da ake ciki.

LABARAI MASU NASABA

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

Yayin da ake fatan ganin sassan biyu sun sake gudanar da tattaunawa ta kai tsaye kuma cikin nasara, wani abun lura shi ne yadda wannan danbarwa ta haifar da mummunan tasiri ga tattalin arzikin duniya baki daya, ba wai kawai kasashen dake shiyyar ta gabas ta tsakiya ba.

Mun dai ga yadda wannan tashin hankali ya gurgunta tsarin gudanar hada-hadar cinikayya na duniya, ciki har da na kasashen yammacin duniya masu karfin ci gaba.

Rufe mashigin Hormuz, ya illata hada-hadar albarkatun makamashi na duniya, wanda hakan ya haifar da hauhawar farashin albarkatun mai a kasuwannin duniya, da tsadar kayayyaki a kusan dukkanin kasashe, ciki har da masu tasowa wadanda da dama can ke cikin yanayi na matsi.

Hakan kuma na da nasaba da yadda makamashi ke da alakar kai tsaye da harkokin sufuri, da sarrafa hajojin masana’antu, da rarraba hajojin zuwa sassan kasa da kasa, da noma, da sayayyar ababen bukatun al’umma na yau da kullum.

Wani muhimmin darasi game da wannan tashin hankali, da ya kai ga rufe mashigin Hormuz, shi ne rashin kwanciyar hankali a wani bangare na duniya, na iya haifar da mummunan tasiri ga duniya baki daya.

Wato dai wannan yaki na gabas ta tsakiya ya zamewa duniya darasi game da muhimmancin tabbatar da zaman lafiya, da walwala a dukkanin sassan kasa da kasa.

Kamar dai yadda Bahaushe kan ce “Zama Lafiya Ya Fi Zama Dan Sarki!”Wannan danbarwa ta zamewa duniya babban kalubale, ta yadda tasirin tashin hankalin na gabas ta tsakiya bai takaita ga yankin kadai ba, maimakon hakan ya haifar da matsalar tattalin arziki da mai yiwuwa a jima ana dandana illar ta. (Saminu Alhassan)

Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana
  • Sulaiman
    Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya
  • Sulaiman
    Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

MASU ALAKA

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya
Daga Birnin Sin

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

June 7, 2026
Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026
Next Post
Tanzania Na Shirin Jan Hankalin Adadi Mai Yawa Na Sinawa Masu Yawon Bude Ido

Tanzania Na Shirin Jan Hankalin Adadi Mai Yawa Na Sinawa Masu Yawon Bude Ido

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

June 8, 2026
Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

June 7, 2026
Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

June 7, 2026
Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.