• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Tabbatar Da Bunkasar Harkokin Rayuwar Al’ummar Gombe In Na Zama Gwamna —Hon Keftin Amuga

by Bello Hamza
3 years ago
in Rahotonni, Manyan Labarai
0
Zan Tabbatar Da Bunkasar Harkokin Rayuwar Al’ummar Gombe In Na Zama Gwamna —Hon Keftin Amuga
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hon. Keftin Amuga, shaharraen dan siyasa ne tun a zamanin jamhoriya ta biyu, kuma kwararre ne a fagen tafiyar da harkokin al’umma shi ne kuma Wakilin Tagale kuma dan takarar neman kujerar gwamnan Jihar Gombe a karkashin jam’iyyar Labour Party (LP), a tattaunawarsa da Mataimakin Editanmu Bello Hamza, ya yi ciakken bayanin yadda zai samar da zama lafiya da bunkasar tattalin arzikin Jihar Gombe tare da tabbatar da adalci.

Ranka ya dade, ko zo ka gabatar mana da kanka

Suna na Hon. Keftin Amoka.

Zamu so mu ji takaitaccen tarihin ka

Ni dai daga Gombe neke, ni kuma Wakilin Tangale a majalisar Jihar Bauchi daga 1979 zuwa 1983. A karkashin jam’iyya Nigeria People’s party (NPN). Ni dai a zamanin mun yi aiki bisa sahihiyar siyasa ba ma siyasar kudi. A lokacin an tabbatar da ayyuka wanda na yi da suka hada da ‘Federal Gobernment College Gardin Sarki. Lokacin Hakimi ne aka bashi sanda tun zamanin, mun samar da su Nitel, Rijiyoyin Burtsatse da sauran ayyukan more rayuwa ga al’umm. A ilmance kuma na yi karatun sakandare a ‘Gobernment College Kaduna’ daga 1968 zuwa 1972. Na tafi ABU Zaria (SBS) 1973 zuwa 1977. Daga nan na tafi NYSC a Jihar Ondo. Na dawo na kama aiki a Jihar Bauchi. Toh daga nan sai na amshi kiran mutanen mu a kan in zo in tsaya a don wakiltarsu a majalisa.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba

Ranka ya dade ganin cewa kana daya daga cikin ‘yan Takaran Gwamna a Jihar Gombe karkashin Jamiyyar LP wato Labour Party me ka tanadar wa al’ummar Jihar Gombe in ka kai ga nasara?

Na farko shi ne tabbatar da zaman lafiya da daidaita zamantakewar al’umma. Domin in babu zaman lafiya a cikin rayuwar mutane, cigaba da bunkasar kasa ba zai samu ba. Zaman lafiya na da matukar muhimmanci. Domin wannan duk wani abu na ganganci ko na Gwamna wanda zai kawo wariya ya kuma daga hankali a cikin al’umma ba zan yarda dashi ba. Zan kauda shi. Ka ji dai bayanin da na yi a kan maganan Sabon Sarkin Tanga. Gwamnati ta bada umurnin aje a yi zabe majalisa sarakuna suka yi zabe wanda suka sa a gaba shi ne Dakta Musa Idris ya samu kuri’a biyar a ciin kuri’a tara na ‘yan majalisa. Suaran biyu suka samu kuri’a biyu. Bisa ga al’ada kuma yadda aka saba yi. Duk wani wanda ya samu kuri’a mafi tsoka fiye da sauran shi ne ake nadawa. Amma a wannan lokacin da aka turo rahoto sai gwamnati ta dauki sarauta ta ba wanda ya samu kuri’a biyu. Don mene ne haka ya faru? Saboda haka mu maganar bamu taba sanin cewa maganan addini zai raba mu ba. Toh irin wannan abubuwan ba zamu yarda da su ba . Ba zamu yarda ba. Kuma koda na zama gwamna irin wannan halaye na ganganci na rashin gaskiya zamu kawar da su don samar da adalci a tsakanin al’umma.

Ranka ya dade ganin cewa matasa su ne kashin bayan al’umma mene ne gwamnatin ka za ta tanadar musu don rage zaman kashe wando a tsakanin al’umma

Toh ni ko da na tashi ina yaro ban ga matasa suna zama gindin itace ba, ba za ka taba ganin yara suna zama gindin itace ba. Domin me? Domin iyaye ba za su yarda ba. Abin da yake faruwar yanzu da ‘ya’yan mu ba daga sama suka sauko ba suna da iyaye. Mu iyaye mun gaza a cikin aikin kula da yayanmu kamar yadda kakanninmu iyayenmu suka yi mana. A zamanin mu yaushe zaka tsaya kana shan sigari a gaban iyayen ka ko giya, ko kuma kana wucewa da yarinyar ka a gaban iyaye. Amma yanzu zaka ga yara suna yin abin da bai kamata ba amma Iyayen na kallo. To zamu fara daga kan iyayen ne tukun. Mu tabbata kowa yasan. alhakin da ke kansa kafin muje mu tabbatar cewa masu siyar masu da kwayan nan su burtutu dinan zamu tattauna dasu, yaya suke so maganan rayuwa ne? Wannan batu da kyau za mu tattauna da wadannan abubuwan domin akwai illa da yawa akai sannan zamu tambaye su wace sana’a da suke so suyi sai mu taimaka masu.

Wato ranka ya dade mene ne gwamnatin ka ta tanada don bunkasa noma da kiwo wandada sune manyan sana’o’in al’ummar jihar Gombe dama Nijeriya ma baki daya?

Noma shi ne tushen arziki. Saboda haka za mu inganta shi. Za mu inganta shi, kasan duk arzikin Amurka noma ne mu kuma na tabbata kasar Amurka bata fi ni’imar kasar mu ba. Toh tunda yake jama’a sun yarda sun karbi sana’ar nan suna yi kowane lokaci ba a sa su tilas dole ne su yi domin su samu su ciyar ma kansu. Gwamnati za ta shiga ta tallafa masu. Tallafi a kowani lokaci a lokacin da yakamata in taki ne, in maganin feshi, in mene duk wani abunda gwamnati za ta zuba. Gwamnati na za ta zuba a yi taimako a cikin wannan.

Toh ranka ya dade ganin cewa zaku fuskanci jam’iyya mai mulki ya kake ganin zaku wani hanya kuke ganin za ku lashe wannan zaben ganin cewa su suna rike da mulki yanzu.

Na farko kam wannan jam’iyya masu mulki suna mana yakin neman zabe ne da kansu ta hanyatr a ayyukan su da maganganun su suna taimaka mana a yakin meman zabe. Amma duk wanda suke in kaga mutum wanda ya ce zai yi PDP zai dauki kuria’ar sa ya ba da takarar gwamnan APC Toh bai yi da gaskiya Toh mu mun dogara ga Allah kuma muna gani a ayyukan da wadannan manyan jam’iyyun suke yi. A na uku jama’a sun na ji a jikin sun. Sun dandana kuma suna ganin sun yadda yanzu mun yi laifi. Mun yi kuskure da muka zabi wannan guda biyu. Toh ba kudi muke da shi ba. Wani kudi muke dashi? Baza mu taba yarda mu kawo maganar kudi ba domin suna da gwamnati amma ayyukan su da abin da mutane suka wahalar da mutane suka ji a jikin su su ne ‘Campaign a gare mu. Shi zai jawo mana mutane.

Toh ranka ya dade zuwa yanzu ka gamsu da yadda hukumar zabe na INEC ke gudanar da ayyukan ta?

Toh yanzu da maganar zabe kam, Kamar yadda ya faru a Jihar Osun dinnan ta hanyar amfani da na’ura mai kkwakwalwa yanzu babu maganar sace akwati. Babu maganar rubuta sakamakon zaben da ba a yi, ko kuma dangwala kuri’a fiye da daya. Toh tun da yake INEC ina ganin ya kai sau biyu ko sau uku ana sa masu matsa lamba suna kokarin ganin an tabbatar da yin zabe sahihi bay tare da magudi bapressure suyi kokari su koma ga hanyar zabe na kwanan baya. Toh sun yi resisting sun ce ba za su yi ba. Toh sai muce at this point Alhamdulillahi. Shirye-shirye da abun da ake ciki yanzu zai biya bukata a kasar nan baki daya.

Ranka ya dade wani kira kake dashi na musamman ga magoya bayan ka a daidai wannan lokaci?

Muna cikin yaki zaben nan. Wannan zaben 2023 ba kamar zaben da ya wuce ba. Zabe ne na tabbatar da makomar al’umma da kuma kasar Nijeriya. Magoya baya na in akwai abin da yafi komai a duniya tsoro ban tsoro shi ne maganan zaben nan mai zuwa. Ya kamata a nats a yi mai tsafta cikin kwanciyar hankali.

Ranka ya dade daga karshe ko akwai wani bayani da kake so ka yi wa al’umma wanda zuwa yanzu ban tambaye ba?

Bayani na mai sauki ne yakamata ‘an arewa su kawar da banbancin addini da kabilanci don a samu cikakkemn cigaba a dukkan bangarorin rayuiwar al’umma

Ranka ya dade muna godiya

Na gode


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GombeHiraLPSiyasatakaraZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: INEC Ta Nemi Masu Kada Kuri’a Da Su Duba Sunayensu Cikin Wadanda Ta Yi Wa Rajista

Next Post

Gwamnatin Jihar Kebbi Za Ta Biya Kudaden Masu Ritaya Naira Biliyan Uku

Related

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

7 hours ago
Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba

12 hours ago
Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya
Manyan Labarai

Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya

17 hours ago
Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu
Manyan Labarai

Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu

1 day ago
Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ
Tsaro

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

1 day ago
Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

1 day ago
Next Post
Gwamnatin Jihar Kebbi Za Ta Biya Kudaden Masu Ritaya Naira Biliyan Uku

Gwamnatin Jihar Kebbi Za Ta Biya Kudaden Masu Ritaya Naira Biliyan Uku

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.