ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zumunci Mai Dorewa Ne Ke Gina Kyakkyawar Makomar Bil’adama Ta Bai-Daya A Kansa

by Sulaiman
6 days ago
Zumunci

Galibin kasashe suna fara alaka da juna ne sakamakon yarjejeniyar diflomasiyya, amma duk da cewa diflomasiyya a tsakanin Sin da Masar an kafa ta ce a hukumance yau shekaru 70 da suka gabata, alakar al’ummomin kasashen biyu ta girmi hakan nesa ba kusa ba, idan aka yi la’akari da cewa Sin da Masar wayewar kai ce guda biyu da suka ba da gagarumar gudunmawa ga tarihin bil’adama a doron kasa.

Akwai kamanceceniya a tsakanin wayewar kan kasashen biyu idan aka dubi yadda Kogin Nilu ya kasance tushen wayewar kai ta Masar, yayin da kogunan Yangtze da Rawaye su kuma suka taka muhimmiyar rawa wajen bunkasar wayewar kan kasar Sin. Kazalika, idan aka waiwayi kasuwancin hanyar siliki da gano kayayyakin kasar Sin a Fustat, za a kara tabbatar da cewa mu’amalar al’ummomin biyu tana da dogon tarihi.

Saboda haka, lokacin da Masar ta zama kasa ta farko a yankin Larabawa da Afirka da ta kulla huldar diflomasiyya da Jamhuriyar Jama’ar Sin a ranar 30 ga watan Mayun 1956, ba wai an fara wata alaka daga tushe ba ce, abin da aka yi shi ne mayar da wata tsohuwar fahimtar juna tsakanin wayewar kai biyu zuwa dangantakar diflomasiyya ta zamani.

ADVERTISEMENT

Kazalika, yana da matukar ban sha’awa yadda aka ci gaba da yaukaka wannan zumunci har zuwa yau da Shugaba Xi Jinping ke ziyarar aiki a kasar Masar bisa gayyatar shugaban kasar Abdel Fattah El-Sisi, wanda a cikin rubutaccen jawabin da Xi ya bayar, ya tabo batun yadda kasashen biyu suke mara baya ga juna a harkokin kasa da kasa.

Idan ba a manta ba, a lokacin rikicin mashigin Suez na shekarar 1956, Sin ta nuna goyon baya ga matsayin Masar, kuma sannu a hankali dangantakar da ta fara da fahimtar juna ta siyasa ta koma hadin gwiwar tattalin arziki, inda a yau kamfanonin Sin ke taka rawa wajen bunkasa yankin tattalin arziki na Suez.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Hadin gwiwar kasashen biyu ya kai ga fannoni da dama, ciki har da sufuri, fasaha, ilimi, al’adu, raya birane da fasahar sararin samaniya wadanda suka kasance daga cikin misalan da ke nuna cewa dangantakar tana kara samun tagomashi.

Cika shekaru 70 na diflomasiyyar Sin da Masar ya zarce batun amincewar siyasa saboda dadadden zumuntar al’ummunsu, kuma wata dama ce ta sake tambayar abin da wasu manyan wayewar kai biyu masu dadadden tarihi za su iya ginawa cikin hadin gwiwa a karni na 21.

Bugu da kari, abin da ya fara a matsayin cudanyar wayewar kai tun zamanin da, sannan ya koma huldar diflomasiyya a 1956, a halin yanzu yana da damar zama wata muhimmiyar gada mai muhimmanci tsakanin Sin da Masar, har ma da dukkannin kasashen Afirka.

Kuma watakila babban darasin cika shekaru 70 da kulla huldar diflomasiyyar shi ne: zumunci mai dorewa da ake ci gaba da gina kyakkyawar makomar bil’adama ta bai-daya a kansa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Zumunci
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Ceto Matar Tsohon Janar Sa’o’i Bayan An Sace Ta A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.