Dakarun Rundunar Sojin Nijeriya sun ceto Misis Adonkie, matar tsohon Birgediya Janar Basil Adonkie, sa’o’i kadan bayan da wasu ’yan bindiga suka yi garkuwa da ita daga gidanta da ke Abuja.
Rundunar ta bayyana hakan ne a cikin wani rahoton musamman wanda ta mika wa Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN) ranar Laraba.
Rahoton ya ce an yi garkuwa da Misis Adonkie ne da misalin karfe 10:30 na daren ranar 1 ga Satumba, lamarin da ya sa aka tura sojoji domin fara bin sawun masu garkuwar cikin hadin gwiwa.
Rahoton ya kara da cewa sojojin sun samu nasarar ceto matar a kusa da kauyen Angwan-Sabo, yayin da wasu daga cikin sojojin suka ci gaba da bin sawun masu garkuwar da suka tsere.














